Shugaba Muhammadu Buhari Ya Fitittiki Shugaban Hukumar NDDC

Shugaba Muhammadu Buhari Ya Fitittiki Shugaban Hukumar NDDC

  • Shugaba Muhammadu Buhari ya fitittiki shugaban hukumar cigaban Neja Delta yau Alhamis
  • An kafa hukumar NDDC ne don tabbatar da jin dadi da ci gaban al'ummar Neja Delta kadai
  • Hukumar NDDC ta yi fama da lamuran rashawa a shekarun baya-bayan nan abin har ya kai binciken kwa-kwaf

Shugaba Muhammadu Buhari ya sallami shugaban rikon kwarya na hukumar cigaban yankin Neja Delta, watau Niger Delta Development Commission (NDDC), Effiong Akwa.

Har yanzu ba'a bayyana takamamman dalilin cire Effiong ba, riwayar TheNation.

Diraktan yada labarai na ma'aikatar lamuran Neja-Delta, Patricia Deworitshe, a bayyana hakan a jawabin da ya fitar.

Ya bayyana cewa Shugaban kasa zai kafa sabuwar kwamitin shugabannin hukumar kuma za'a sanar da sunayensu daga baya.

DUBA: Bibiyemu a Instagram don samun labarai masu muhimmanci kai tsaye cikin manhajar

Asali: Legit.ng

Online view pixel