Jerin Gwamnoni 4, Ministoci 8, Da Wasu Manya 4 Da Suka Yiwa Buhari Rakiya Amurka

Jerin Gwamnoni 4, Ministoci 8, Da Wasu Manya 4 Da Suka Yiwa Buhari Rakiya Amurka

Shugaba Muhammadu Buhari ya tafi birnin New York, kasar Amruka don halartan taron gangamin majalisar dinkin duniya.

Wakilin kamfanin dillancin labaran Najeriya NAN ya ruwaito cewa Shugaba Buhari ya dira babbar tashar jirgin JF Kennedy ne misalin karfe 6:20 na yamma.

Shugaban kasan ya samu tarba daga wajen Ministan harkokin wajen Najeriya, Geoffrey Onyeama; wakilin Najeriya a majalisar dinkin duniya, Tijjani Muhammad-Bande da jakadan Najeriya zuwa Amurka, Dr Mrs Uzoma Emenike, dss.

Shugaba Buhari zai gabatar da jawabin farko na ranar Laraba ga shugabannin duniya misalin karfe 2 na rana (agogon Najeriya).

Buhari
Jerin Gwamnoni 4, Ministoci 8, Da Wasu Manya 4 Da Suka Yiwa Buhari Rakiya Amurka Hoto: Buhari Sallau
Asali: Facebook

Legit.ng Hausa ta tattaro muku jerin wadanda suka raka Buhari New York

Gwamnoni

DUBA: Shigo shafin Legit.ng na manhajar Legit.ng na Telegram! Kada ka bari komai ya wuce ka

Kara karanta wannan

Sunayen Tsofaffin Shugabannin Rundunar Soji Uku da Zasu Yi Wa Atiku Kamfe a 2023

Gwamnan jihar Borno, Babagana Umara Zulum

Gwamnan jihar Zamfara, Muhammadu Bello Matawalle

Gwamnan CBN, Godwin Emefiele

Gwamnan jihar Legas, Babajide Sanwoolu

Ministoci

Ministan Aikin Noma, Mahmoud Mohammed

Ministan masana'antu da kasuwanci, Otunba Niyi Adebayo

Ministan Ilimi, Adamu Adamu

Ministan Sufuri Muazu Jaji

Ministan Lafiya, Osagie Ehanire

Ministan harokin wajen Najeriya, Geofreey Onyeam

Ministar Jinkai, Walwala da jin dadin al'umma Sadiya Farouq

Ministar Kudi, Zainab Shamsuna

Saura

Shugaban ma'aikatan fadar shugaban kasa, Farfesa Ibrahim Gambari

Tsohon Sakataren gwamnatin tarayya, Babagana Kingibe

Shugaban hukumar EFCC, AbdulRashid Bawa

Shugabar hukumar NIDCOM, Abike Dabiri

Mai Baiwa shugaban kasa kan tsaro, Babagana Munguno

Mai Magana da Yawun shugaban kasa, Femi Adesina

Asali: Legit.ng

Tags:
Online view pixel