Bayan yan makonni 3 da Sulhu, Isra'ila ta sake kaiwa Falasdinawa hari

Bayan yan makonni 3 da Sulhu, Isra'ila ta sake kaiwa Falasdinawa hari

• Jirgin yaki ya kaddamar da sababbin hare-hare a kan yankunan da mayakan Hamas ke zaune a Zirin Gaza

• Sojoji sun ce martani ne ga ababen fashewa da Hamas ta harba zuwa Kudancin Isra’ila

• Isra’ila ta ce tana cikin shirin duk wani martanin da za a mayar ko da sabon yaki ne

Jiragen yakin sojin Isra’ila sun kaddamar da sababbin hare-hare kan kungiyar Hamas a Zirin Gaza, wanda hakan ya kawo karshen takaitaccen tsagaita wutar da aka cimma bayan mummunan fadan da ya barke a yankin a baya bayan nan.

Wata sanarwa da rundunar tsaron Isra'ila IDF ta fitar, ta ce jiragen yakinta sun kai hare-hare kan wasu gine-gine na rundunar da ke kare yankin Khan Yunis a cikin birnin Gaza, rahoton Daily Mail.

Ta kuma ce ayyukan ta'addanci na aukuwa a wadannan wuraren, kuma rundunar a shirye take ta tunkari dukkan martanin da zai biyo baya, wadanda suka hada da ci gaba da kai hari a Zirin Gaza.

Sojojin Isra'ilar sun harba rokokin kan Gazan a mastayin ramuwar gayya, bayan tashin gobara a yankunanta da dama sakamakon ababen fashewa da kungiyar Hamas ta harba.

Bayan yan makonni 3 da Sulhu, Isra'ila ta sake kaiwa Falasdinawa hari
Bayan yan makonni 3 da Sulhu, Isra'ila ta sake kaiwa Falasdinawa hari
Source: UGC

A karon farko tun bayan kawo karshen rikicin kwanaki 11 a zirin Gaza, wanda ya yi sanadiyar mutuwar Falasdinawa sama da 200, Isra'ila ta kaddamar da hare-haren ramuwar gayya zuwa zirin gaza, bayan da kungiyar Hamas ta harba balam-balam masu fashewa da suka haddasa gobara a wasu yankunan Isra'ilar.

Matakin ya biyo bayan wani maci da Yahudawa masu tsanannin kishin kasa suka yi a yankin gabashin birnin Qudus a ranar Talatar nan, wanda ya haifar da kakkausar suka daga kungiyar Hamas,da ita ce kungiyar da ke iko da yankin na Gaza a hukumance, riwayar France24.

Sai dai ba a tabbatar ko akwai wadanda wannan harin ya jikkata ba.

Falasadinawa sun lashi takobin kwato Kudus

Wani kakakin Hamas ya fitar da wata sanarwa a Twitter yana cewa Falasdinawa za su ci gaba da "jajircewar da suke yi da kare 'yancinsu da yankuna masu tsarki" a birnin Qudus.

Hukumar kashe gobara ta Isra'ila ta ce balan-balan din da mayakan Hamas suka harba sun haifar da gobara kimanin 20 a wasu yankunan Kudancin Isra'ila.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdul Rahman Rashid avatar

Abdul Rahman Rashid Rashidah Abdul Rahman 'yar jarida ce kuma dalibar ilimi wacce ta kwashe shekaru kimanin hudu yanzu tare da shararriyar jarida Legit. Ta samu gogewa a ɓangaren rubutun labarai akan fannoni shatta, wanda suka hada da siyasa, kasuwanci, wasanni, nishadi, dss. Zaku tuntubarta a akwatin email: abdulrahman.rashidah@corp.legit.ng