Jerin wadanda suka rike mukamin shugaban hukumar EFCC a tarihin Najeriya

Jerin wadanda suka rike mukamin shugaban hukumar EFCC a tarihin Najeriya

Hukumar hana almundahana da yiwa tattalin arzikin kasa zagon kasa watau EFCC na daya daga cikin hukumomin yaki da rashawa biyu dake Najeriya tun komawarta demokridayya a 1999.

Hukumar na da alhakin binciken ha'inci da almundahanan kudi da ma'aikatan gwamnati, hakazalika masu damfarar mutane.

A kwanakin bayan nan, hukumar ta samu nasarori da dama wajen kama yan damfarar yanar gizo wadanda akafi sani da 'yahoo boys'.

Cif Olusegun Obasanjo ne ya kafa hukumar EFCC a shekarar 2003 domin yakan jami'an gwamnatin Najeriyan da suka sace dukiyan al'umma.

Legit ta kawo muku jerin wadanda suka jagoranci wannan hukumar daga 2003 zuwa yanzu:

Nuhu Ribadu (2003 - 2007)

Farida Waziri (2008 - 2011)

Ibrahim Lamorde (2011 - 2015)

Ibrahim Magu (Mukaddashi 2015 -2020)

Mohammed Abba (Mukaddashi 2020 - 2021)

Abdulrasheed Bawa (Mukaddashi 2021 - Kawo yanzu)

KU KARANTA: Jimoh Ibrahim: Attajirin da Gwamnatin Buhari ta karbewa kadarori ya gaza dawo da su ta kotu

Jerin wadanda suka rike mukamin shugaban hukumar EFCC a tarihin Najeriya
Jerin wadanda suka rike mukamin shugaban hukumar EFCC a tarihin Najeriya credit: @OfficialEFCC
Asali: Twitter

DUBA NAN: Yan majalisar wakilan tarayya 2 sun sauya sheka zuwa jam'iyyar APC

Yawancin wadannan mutane da suka rike wannan hukuma basu kammala wa'adinsu ba face an dakatad da su ana zarginshi da wani laifi.

Na karshe-karshe shine Ibrahim Magu wanda gwamnatin shugaba Buhari ta dakatad kan zargin sayarwa abokansa dukiyoyin da hukumar ta kwace daga hannun barayin gwamnati.

Har yanzu, ba'a gurfanar da Ibrahim Magu a kotu don amsa wannan laifi ba.

An bukaci shugaba Muhammadu Buhari da ya gabatar da rahoton kwamitin shari’a kan tsohon Mukaddashin Shugaban Hukumar EFCC, Ibrahim Magu.

A cikin wata wasika da aka aika wa shugaban, babbar kungiyar kawancen yaki da cin hanci da rashawa ta duniya ta nuna matukar damuwar cewa an tsoma bakin siyasa a cikin aikin EFCC.

Ta kuma bayyana gazawar mahukuntan Najeriya wajen fitar da rahoton dake da alhakin faduwar Najeriya a kwanan nan a shirin yaki da cin hanci da rashawa da kungiyar Transparency International ta yi.

Asali: Legit.ng

Online view pixel