Adadin masu cutar korona a Najeriya ya zarta 47,000 - NCDC
Babu shakka mahukuntan lafiya na ci gaba da fadi tashin dakile yaduwar cutar korona a Najeriya, sai dai fa lamarin ya ci tura domin kuwa cutar na ci gaba da bazuwa babu sassauci.
A halin yanzu an samu bullar cutar covid-19 a duk jihohi 36 na Najeriya da kuma babban birnin tarayya kamar yadda alkaluman cibiyar dakile yaduwar cututtuka a kasar NCDC suka tabbatar.
Taskar bayanai ta NCDC a ranar Laraba, 12 ga watan Agustan 2020, ta sanar cewa cutar korona ta harbi mutane 47,743 yayin da mutum 33,943 suka samu waraka.

Asali: Twitter
Ya zuwa yanzu dai mutane 956 cutar ta hallaka a fadin Najeriya kamar yadda hukumar NCDC ta fidda bayanan alkalumanta.
Rumbun tattaro bayanai na NCDC ya nuna cewa, an yi wa mutum 338,084 gwajin cutar a duk fadin kasar tun bayan bullarta karo na farko a ranar 27 ga watan Fabrairun 2020.
Haka kuma alkaluman cibiyar dakile cututtuka ta kasar sun nuna cewa, mutum 12,844 ne suka rage masu dauke da kwayoyin cutar.
KARANTA KUMA: Bayan yi wa Sarki Salman tiyata, an garzaya da shi yankin Bahar Maliya inda zai huta
Da misalin karfe 11.29 na jiya Laraba da daddare, NCDC ta sanar da cewa an gano karin sabbin mutane 453 da cutar ta harba a fadin Najeriya.
Sabbin mutane 453 da cutar ta harba cikin jihohi 16 sun kasance kamar haka:
Lagos(113), Abuja(72), Filato(59), Enugu(55), Kaduna(38), Ondo(32), Osun(26), Ebonyi(20), Ogun(9), Delta(8), Borno(7), Akwa Ibom(6), Oyo(5), Bauchi(1), Kano(1) da Ekiti(1).
Har kawo yanzu jihar Legas ce a kan sahu na gaba ta fuskar yawan mutanen da cutar ta harba, sai kuma birnin Abuja a mataki na biyu yayin da jihar Oyo ta biyo bayansu a mataki na uku.
Ga jerin adadin mutanen da cutar ta harba cikin kowace daya daga cikin jihohi 36 na Najeriya da cutar ta bulla:
Lagos - 16,187
Abuja - 4,597
Oyo - 2,895
Edo - 2,399
Ribas - 1,972
Kaduna 1,666
Kano - 1,644
Filato - 1,643
Delta - 1,621
Ogun - 1,506
Ondo - 1,356
Enugu - 969
Ebonyi - 908
Kwara - 882
Katsina - 746
Borno - 697
Osun - 678
Abia - 663
Gombe - 635
Bauchi - 579
Imo - 485
Benue - 430
Nasarawa - 371
Bayelsa - 346
Jigawa - 322
Akwa Ibom - 241
Niger - 226
Ekiti - 194
Adamawa - 185
Anambra - 156
Sokoto - 154
Kebbi - 90
Taraba - 78
Zamfara - 77
Cross River - 73
Yobe - 67
Kogi - 5
Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:
https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/legitnghausa
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,
Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Asali: Legit.ng