Adadin masu cutar korona a Najeriya ya zarta 20, 000 - NCDC

Adadin masu cutar korona a Najeriya ya zarta 20, 000 - NCDC

A yanzu kusan watanni hudu kenan bayan bullar cutar korona karo na farko a Najeriya, cutar mai toshe kafofin numfashi ta yadu a jihohi 35 na kasar da babban birnin kasar na Tarayya wato Abuja.

Wannan ya na kunshe cikin kididdigar alkaluman da Hukumar Dakile Cututtuka Masu Yaduwa a Najeriya NCDC ta fitar a daren ranar Litinin, 22 ga watan Yuni.

Har ila yau dai jihar Cross River ce kadai ba a samu bullar cutar ba a duk fadin kasar, sai da masu ruwa da tsaki sun ce rashin kayan aiki da karancin ma'aikatan lafiya ya yi tasiri a kan lamarin.

A yayin da likafar cutar ke ci gaba babu sassauci, har yanzu jihar Legas ce ke jan ragama ta yawan masu cutar inda ta harbi mutum 8,864, sai kuma mutum 1,448 da suka warke, yayin da mutum 126 suka kwanta dama.

Kawo yanzu a duk fadin Najeriya, cutar ta harbi mutum 20,919, sai kuma mutum 7,109 da suka samu waraka, yayin da mutum 525 suka riga mu gidan gaskiya.

Shugaban NCDC; Chikwe Ihekweazu
Shugaban NCDC; Chikwe Ihekweazu
Asali: Twitter

Taskar bayanai ta NCDC ta nuna cewa, an yi wa mutum 117,569 gwajin cutar a duk fadin kasar tun bayan bullarta karo na farko a ranar 27 ga watan Fabrairu.

Haka kuma alkaluma Cibiyar dakile cututtuka ta kasar sun nuna cewa, mutum 13,285 ne suka rage masu dauke da kwayoyin cutar.

Da misalin karfe 11.14 na ranar Litinin da daddare, NCDC ta sanar da cewa an gano karin sabbin mutane 675 da cutar ta harba a fadin Najeriya.

Sabbin mutane 436 da cutar ta harba cikin jihohin 19 sun kasance kamar haka: Lagos(288), Oyo(76), Rivers(56), Delta(31), Ebonyi(30), Gombe(28), Ondo(20), Kaduna(20), Kwara(20), Ogun(17), FCT(16), Edo(13), Abia(10), Nasarawa(9), Imo(9),Bayelsa(8), Borno(8), Katsina(8), Sokoto(3), Bauchi(3), Plateau(2).

Baya ga jihar Legas da ta ke kan sahu na gaba ta fuskar yawan mutanen da cutar ta harba, birnin Abuja ya biyo bayanta a mataki na biyu yayin da jihar Kano ta biyo bayansu a mataki na uku.

Ga jerin adadin mutanen da suka kamu da cutar a kowace daya daga cikin jihohi 35 na Najeriya da ta bulla:

  1. Lagos - 8,864
  2. FCT - 1,583
  3. Kano - 1,190
  4. Oyo - 988
  5. Rivers - 930
  6. Edo - 797
  7. Ogun - 663
  8. Kaduna - 600
  9. Delta - 532
  10. Gombe - 479
  11. Borno - 476
  12. Bauchi - 467
  13. Katsina - 434
  14. Jigawa - 317
  15. Ebonyi - 264
  16. Plateau - 253
  17. Imo - 243
  18. Abia - 232
  19. Kwara - 200
  20. Nasarawa - 193
  21. Bayelsa - 177
  22. Ondo - 154
  23. Enugu - 144
  24. Sokoto - 138
  25. Zamfara - 76
  26. Kebbi - 67
  27. Anambra - 66
  28. Niger - 66
  29. Akwa Ibom - 65
  30. Osun - 60
  31. Yobe - 56
  32. Adamawa - 45
  33. Benue - 44
  34. Ekiti - 35
  35. Taraba - 18
  36. Kogi - 3

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng