Yanzu-yanzu: Babban lauyan Najeriya, Badejo, ya yanke jiki ya fadi ya mutu

Yanzu-yanzu: Babban lauyan Najeriya, Badejo, ya yanke jiki ya fadi ya mutu

- Najeriya ta yi rashin manyan lauyoyi biyu a ranar Juma'a; Sir Jadegoke Adebonajo Badejo (SAN) da Sir Alfred Oghogho Eghobamien

- Badejo ya yanke jiki ya fadi yayin da yake fita daga gidansa a ranar Juma'a dom zuwa wurin aiki

- A yau Asabar, 6 ga watan Yuni ne kungiyar manyan lauyoyin Najeriya ta sanar da mutuwar a wata takardar ta'aziyya da ta fitar

Jadegoke Adebonajo Badejo babban lauyan Najeriya ne wanda ya yanke jiki ya fadi a yayin da yake fita daga gidansa a ranar Juma'a, 5 ga watan Yuni.

Badejo shine babban mai hannun jari a Bonajo Badejo & Co, ya rasu yana da shekaru 61 a duniya, jaridar The Nation ta ruwaito.

"Ya shirya tsaf don fita daga gida. Yana kokarin fita aiki ne a jiya da ya yanke jiki ya fadi kuma ya mutu a take," in ji wata majiya da ta bukaci a sakaya sunanta.

Legit.ng ta gano cewa, Badejo ya kammala karatunsa na zama babban lauya a 1980.

Ya kammala digirinsa na farko a jami'ar Ife wacce a yanzu ake kira da jami'ar Obafemi Awolowo da kuma digirinsa na biyu a jami'ar jihar Legas.

A dayan bangaren, Alfred Oghogho Eghobamien ya rasu a ranar Juma'a yana da shekaru 85.

Eghobamien mahaifi ne ga Osaro Eghobamien wanda shi ma babban lauya ne.

Yanzu-yanzu: Babban lauyan Najeriya, Badejo, ya yanke jiki ya fadi ya mutu
Yanzu-yanzu: Babban lauyan Najeriya, Badejo, ya yanke jiki ya fadi ya mutu. Hoto daga The Nation
Asali: UGC

KU KARANTA: Sabon tsarin Facebook: Yadda zaka rika ganin labaran Legit.ng Hausa a shafinka da dumi-dumi

Ya zama cikakken lauya a shekarar 1972. Ya samu mukamin zama babban lauyan Najeriya a 1995.

A yau Asabar, 6 ga watan Yunin 2020 ne kungiyar manyan lauyoyin Najeriya ta fitar da sanarwa dauke da ta'aziyyar mutuwarsu.

A ta'aziyyar Badejo, sakataren BOSAN, Seyi Sowemimo ya ce: "Muna jimamin sanar da mutuwar abokin aikinmu. Muna fatan Ubangiji ya bai wa iyalansa hakurin jure rashinsa.

"Shirye-shiryen birneshi zasu fito daga iyalansa kuma za a sanar."

A yayin jajanta mutuwar Eghobamien, Ya ce: "A matsayinsa na babban lauya a harkar siyasar jihar Edo, Eghobamien ya wakilci jihar a taron CONFAB na 2005."

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel