Yanzu-yanzu: Babban lauyan Najeriya, Badejo, ya yanke jiki ya fadi ya mutu

Yanzu-yanzu: Babban lauyan Najeriya, Badejo, ya yanke jiki ya fadi ya mutu

- Najeriya ta yi rashin manyan lauyoyi biyu a ranar Juma'a; Sir Jadegoke Adebonajo Badejo (SAN) da Sir Alfred Oghogho Eghobamien

- Badejo ya yanke jiki ya fadi yayin da yake fita daga gidansa a ranar Juma'a dom zuwa wurin aiki

- A yau Asabar, 6 ga watan Yuni ne kungiyar manyan lauyoyin Najeriya ta sanar da mutuwar a wata takardar ta'aziyya da ta fitar

Jadegoke Adebonajo Badejo babban lauyan Najeriya ne wanda ya yanke jiki ya fadi a yayin da yake fita daga gidansa a ranar Juma'a, 5 ga watan Yuni.

Badejo shine babban mai hannun jari a Bonajo Badejo & Co, ya rasu yana da shekaru 61 a duniya, jaridar The Nation ta ruwaito.

"Ya shirya tsaf don fita daga gida. Yana kokarin fita aiki ne a jiya da ya yanke jiki ya fadi kuma ya mutu a take," in ji wata majiya da ta bukaci a sakaya sunanta.

Legit.ng ta gano cewa, Badejo ya kammala karatunsa na zama babban lauya a 1980.

Ya kammala digirinsa na farko a jami'ar Ife wacce a yanzu ake kira da jami'ar Obafemi Awolowo da kuma digirinsa na biyu a jami'ar jihar Legas.

A dayan bangaren, Alfred Oghogho Eghobamien ya rasu a ranar Juma'a yana da shekaru 85.

Eghobamien mahaifi ne ga Osaro Eghobamien wanda shi ma babban lauya ne.

Yanzu-yanzu: Babban lauyan Najeriya, Badejo, ya yanke jiki ya fadi ya mutu
Yanzu-yanzu: Babban lauyan Najeriya, Badejo, ya yanke jiki ya fadi ya mutu. Hoto daga The Nation
Asali: UGC

KU KARANTA: Sabon tsarin Facebook: Yadda zaka rika ganin labaran Legit.ng Hausa a shafinka da dumi-dumi

Ya zama cikakken lauya a shekarar 1972. Ya samu mukamin zama babban lauyan Najeriya a 1995.

A yau Asabar, 6 ga watan Yunin 2020 ne kungiyar manyan lauyoyin Najeriya ta fitar da sanarwa dauke da ta'aziyyar mutuwarsu.

A ta'aziyyar Badejo, sakataren BOSAN, Seyi Sowemimo ya ce: "Muna jimamin sanar da mutuwar abokin aikinmu. Muna fatan Ubangiji ya bai wa iyalansa hakurin jure rashinsa.

"Shirye-shiryen birneshi zasu fito daga iyalansa kuma za a sanar."

A yayin jajanta mutuwar Eghobamien, Ya ce: "A matsayinsa na babban lauya a harkar siyasar jihar Edo, Eghobamien ya wakilci jihar a taron CONFAB na 2005."

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng