Babbar magana: Wallahi sai na kashe mahaifiyata sannan na kashe kaina, saboda na kamata dumu-dumu tana zina da saurayina
- Wata budurwa ta koka akan abinda mahaifiyarta da saurayinta suka yi mata
- Budurwar ta bayyana cewa ta dawo daga coci tana shiga gidansu ta iske saurayinta kwance da mahaifiyarta
- Ta kara da cewa wallahi yanzu sai ta kashe mahaifiyarta sannan ta kashe kanta
Mahaifiyata na kwanciya da saurayina, ko kuma nace saurayinmu. Mahaifina yana nan da ranshi, amma kuma ba shi da lafiya. Na kai mata saurayina suka gaisa bayan ya bayyana cewa zai aureni.
Har ce mini yayi shi talaka ne, amma duk da haka nace mishi ina son shi zan aure shi tunda har yana da aiki mai kyau kuma zai iya kula dani.
Saurayia ya zo garin mu jiya, sai na roke shi akan cewa ba zan bari ya kama otel ba, nace mishi ya zo gidanmu ya kwana, na gyara mishi daki daya a gidanmu, dawowar da zanyi daga coci da yamma sai na iske mahaifiyata a kanshi.
KU KARANTA: Tashin hankali: Likitoci sun ciro cokula guda 20 a cikin wani mutumi marar lafiya
Ni dai gani nan ne kawai, ina tafiya ne kawai ban ma san mene yake yi mini dadi ba. Menene ya kamata nayi? Abinda yafi bani mamaki ma shine saurayina baya son mata masu kiba, amma daga yaya har yaji mahaifiyata tayi masa.
Na tsani mahaifiya wallahi, zan kashe mahaifiyata na kashe kaina kowa ma ya huta, ba zan taba iya cigaba da zama da wannan bakin cikin ba.
Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.
Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu:
https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/legitnghausa
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,
Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Asali: Legit.ng