Ai ka ji irin ta: Sadiya, tsaleliyar budurwa, ta bata bayan ta tafi ganin saurayi da suka hadu a dandalin sada zumunta (Hotuna)
'Yar uwa ga wata kyakyawar budurwa da ake nema tsawon kwanaki biyar ta nemi taimakon jama'a a kan su taya ta cigiya.
A cewar ta, 'yar uwarta mai matsakaitan shekaru ta bata ne bayan haduwa da wani saurayi a dandalin sada zumunta.
Kyakyawar matashiyar da bata fi shekaru 20 a duniya ta bar gida ne tare da wani saurayi da suka hadu a dandalin 'Facebook', amma har yanzu bata dawo gida ba, kuma wayarta a kashe.
A wani sako da ta wallafa a shafinta na 'Facebook' tare da hoton matashiyar, 'yar uwarta ta bayyana cewa, "'yar uwata, Sadiya, ta bata a garin Jos kimanin kwanaki biyar da suka gabata. Ta hadu da wani saurayi a dandalin sada zumunta, a saboda haka ta bar gida da safe. Bayan ta fita ne sai kawarta ta zo nemanta, tun lokacin aka kira wayarta amma sai muka ji a kashe kuma har yanzu lambarta bata shiga. Don Allah ku taya ni addu'a Allah ya bayyana ta cikin rai da koshin lafiya."

Asali: Facebook
DUBA WANNAN: Arziki: Salah ya nuna motocinsa masu tsada, har da ta naira biliyan 70

Asali: Facebook
Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.
Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/legitnghausa
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,
Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Asali: Legit.ng