Yadda wani Fasto ya yiwa mata 20 ciki a cocinsa

Yadda wani Fasto ya yiwa mata 20 ciki a cocinsa

Jami’an yan sanda reshen jihar Enugu sun kama wani fasto bisa laifin yi ma mambobin cocinsa su 20 ciki.

Faston mai shekara 53 mai suna Timothy Ngwu ya kasance babban mai kula da cocin Vineyard Ministry of the Holy Trinity dake Enugu.

An rahoto cewa yayi ikirarin cewa ruhu mai tsarki ya bashi umurni da yayi ma mambobin cocinsa mata ciki.

Kakakin rundunar yan sandan Enugu, Ebere Amaraizu ya bayyana cewa an gurfanar da faston bisa laifin keta hakki.

Yadda wani Fasto ya yiwa mata 20 ciki a cocinsa
Yadda wani Fasto ya yiwa mata 20 ciki a cocinsa
Asali: UGC

Majiya kusa da cocin faston sun bayyana cewa faston yana ikirarin cewa yana biyayya ne ga umurnin ruhu da ya aikata abunda Allah yayi umurni, ba tare da yin la’akari da ko suna da aure ko basu da aure ba.

Majiyinmu ya cigaba da bayyana cewa a duk lokacin da wadanda yayi ma cikin suka haifi yara, ana barin yaran da iyayensu mata a cocin har karshen rayuwarsu.

An tattaro cewa an matarsa ce ta kai karar faston ga yan sanda bayan ta gaji da mugun aikin da yake tafkawa bayan ya yiwa yar uwarta ciki duk cikin umurnin ‘biyayya ga Ubangiji’.

KU KARANTA KUMA: Osinbajo ya yabawa Saraki a kan wani abu daya da yayi a kan mulki

Yayin da yake kare kansa, faston ya bayyana cewa, har ila yau, bai taba saduwa da kowanne daga cikin matan ba face da amincewa akan bukatan ruhu.

Haka zalika, an dauko daga bakin shi yana fadin cewa yana da mata biyar da yara 13 tare da kwarkwara da dama wadanda ya samu bayan umurnin da ‘ruhu ya bashi’.

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewa tare da mu.

Ga masu bukatar manhajar mu na Azumi a wannan wata mai albarka sai a bibiyi wannan shafi https://fb.gg/play/ramadan_ramadan

Asali: Legit.ng

Online view pixel