Yanzu-yanzu: El-Rufa'i ya yi arangama da masu garkuwa da mutane a hanyar Abuja

Yanzu-yanzu: El-Rufa'i ya yi arangama da masu garkuwa da mutane a hanyar Abuja

Gwamnan jihar Kaduna, Nasir Ahmad El-Rufa'i ya yi arangama da masu garkuwa da mutane yayinda suke kokarin sace matafiya a hanyar Kaduna zuwa Abuja da ranar Laraba, 3 ga watan Afrilu, 2019.

Wani jawabin da mai magana da yawun gwamna, Samuel Aruwan, ya saki ya nuna cewa a ranar Laraba, gwamnan ya nufi birnin tarayya Abuja sai ya isa kauyen Akilubu misalin karfe 3:40 na rana, kawai sai ya hagi tarun motoci kan hanya inda sukace masu garkuwa da mutane na kan gaba.

KU KARANTA: Majalisar Shari'a ta yanke shawara kan Walter Onnoghen, ta aikewa Buhari wasika

Yace: "Jami'an tsaron gwamnan sun kawar da masu garkuwa da mutanen wadanda suka arce cikin daji."

"Bayan bude hanyar, gwamna El-Rufa'i ya bada umurnin cewa wadanda yan bindigan suka jiwa rauni a kaisu asibiti da gaggawa."

"Kana gwamnan ya umurci jami'an tsaro su tsananta sintiri a hanyar domin kawar da yan barandan."

Mun kawo muku rahoton cewa sakamakon hare-hare da garkuwa da mutanen da ya addabi babban hanyar Abuja zuwa Kaduna da kuma Kaduna zuwa Birnin gwari, majalisar tsaron jihar Kaduna ta yanke shawaran karfafa sintiri a hanyoyin domin rage hare-haren.

Masu garkuwa da mutane sun dawo hanyar Kaduna zuwa Abuja da kuma hanyar birnin gwari. Tsakanin ranar Lahadi da Litinin kadai, an yi garkuwa da akalla mutane 42.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng