Yanzu-yanzu: El-Rufa'i ya yi arangama da masu garkuwa da mutane a hanyar Abuja
Gwamnan jihar Kaduna, Nasir Ahmad El-Rufa'i ya yi arangama da masu garkuwa da mutane yayinda suke kokarin sace matafiya a hanyar Kaduna zuwa Abuja da ranar Laraba, 3 ga watan Afrilu, 2019.
Wani jawabin da mai magana da yawun gwamna, Samuel Aruwan, ya saki ya nuna cewa a ranar Laraba, gwamnan ya nufi birnin tarayya Abuja sai ya isa kauyen Akilubu misalin karfe 3:40 na rana, kawai sai ya hagi tarun motoci kan hanya inda sukace masu garkuwa da mutane na kan gaba.
KU KARANTA: Majalisar Shari'a ta yanke shawara kan Walter Onnoghen, ta aikewa Buhari wasika
Yace: "Jami'an tsaron gwamnan sun kawar da masu garkuwa da mutanen wadanda suka arce cikin daji."
"Bayan bude hanyar, gwamna El-Rufa'i ya bada umurnin cewa wadanda yan bindigan suka jiwa rauni a kaisu asibiti da gaggawa."
"Kana gwamnan ya umurci jami'an tsaro su tsananta sintiri a hanyar domin kawar da yan barandan."
Mun kawo muku rahoton cewa sakamakon hare-hare da garkuwa da mutanen da ya addabi babban hanyar Abuja zuwa Kaduna da kuma Kaduna zuwa Birnin gwari, majalisar tsaron jihar Kaduna ta yanke shawaran karfafa sintiri a hanyoyin domin rage hare-haren.
Masu garkuwa da mutane sun dawo hanyar Kaduna zuwa Abuja da kuma hanyar birnin gwari. Tsakanin ranar Lahadi da Litinin kadai, an yi garkuwa da akalla mutane 42.
Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.
Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu:
https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/legitnghausa
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,
Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Asali: Legit.ng