Tiryan-tiryan: Jerin rumfunan mazabun da za'a sake kada kuri'a a zaben gwamnan Kano
Bayan kammala tattara sakamakon zaben kananan hukumomi 44 na jihar Kano, hukumar zabe ta kasa mai zaman kanta wato INEC, ta kaddamar da cewa sai an sake gudanar da zabe a mazabun wasu kananan hukumomi na jihar.
Kamar yadda shafin jaridar Daily Trust ya ruwaito, babban Bature kuma Kwamishinan zabe na jihar Kano, Farfesa Riskuwa Shehu shine ya bayyana hakan a daren yau na Litinin cikin hedikwatar INEC da ke birnin Kanon Dabo.
KU KARANTA: Hukumar INEC ta sa akama jami'in ta a Imo
A cewar sa, dan takarar kujerar gwamnan jihar na jam'iyyar PDP, Abba Kabir Yusuf, ya samu gamayyar kuri'u 1,014,474 yayin da dan takara na jam'iyyar APC, Gwamna Abdullahi Umar Ganduje, ya samu kuri'u 987,819.
Ga dai jerin Tiryan-tiryan: Jerin rumfunan mazabun da za'a sake kada kuri'a a zaben gwamnan:
Bichi: Rumfar zabe daya
Dawakin Kudu: Rumfar zabe daya
Doguwa: Rumfunan zabe 8
Gabasawa: Rumfunan zabe 5
Gezawa: Rumfar zabe 1
Sumaila: Rumfunan zabe 3
Warawa: Rumfunan zabe 3
Kiru: Rumfar zabe 1
Rimin Gado: Rumfar zabe 1
Wudil: Rumfar zabe 3
Tudun Wada: Rumfar zabe 4
Minjibir: Rumfar zabe 10
Rogo: Rumfar zabe 4
Kura: Rumfar zabe 1
Takai: Rumfar zabe 4
Kano Municipal: Rumfar zabe 4
Nassarawa: Ana tababar yawan rumfunan lokacin wannan rahoton
Dala: Ana tababar yawan rumfunan lokacin wannan rahoton
Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma legit.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.
Latsa wannan domin samun labarai a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://web.facebook.com/legitnghausa?_rdc=1&_rdr
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,
Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.com
Asali: Legit.ng