Kishin-kishin: Jaruma Nafisa Abdullahi ta kusa zama amarya

Kishin-kishin: Jaruma Nafisa Abdullahi ta kusa zama amarya

A cigaba da kawo maku labaran masana'antar shirya fina-finai ta Hausa wata Kanny wood, yau mun leko maku wani labari da ke ta yawo a masana'antar na cewa daya daga cikin fitattun fuskokin ta watau jaruma Nafisa Abdullahi na daf da zama amarya.

Wannan kishin-kishin din dai ta soma ne tun daga lokacin da jarumar ta je a shafin ta na dandalin sadarwar zamani na Tuwita ta rubata cewa "Yanzu ta tabbata" da turanci watau "It's official" sannan kuma ta sa alamar zobe.

Kishin-kishin: Jaruma Nafisa Abdullahi ta kusa zama amarya
Kishin-kishin: Jaruma Nafisa Abdullahi ta kusa zama amarya
Asali: UGC

KU KARANTA: Mai da'awar annabtar da yayi hasashen faduwar Buhari ya sake magana

Wannan dai kamar yadda muka samu, ya haifar da doguwar muhawara a shafin na ta inda mutane masu bibiyar ta suka yi ta yi mata Allah ya sa alheri da sauran addu'oi dai irin na masoya.

Sai dai kuma dukka a cikin muhawarar da aka tafka a kasar rubutun nata ciki kuwa hadda masu tambayar ta karin haske ko gaskiyar abun da ta rubuta, jarumar bata ba kowa ansa ba. Bata ce e da gaske ne ba ba kuma ta ce ba gaskiya bane ba.

Mai karatu dai zai iya tuna cewa a kwanan baya jarumar ta yi soyayya mai karfi da jarumi Adam Zango da har ma aka rika tunanin za suyi aure amma sai suka bata daga baya.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma legit.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun labarai a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://web.facebook.com/legitnghausa?_rdc=1&_rdr

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.com

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng