Wata-sabuwa: An yi zina da ma'aikatan mu lokacin zaben shugaban kasa - INEC

Wata-sabuwa: An yi zina da ma'aikatan mu lokacin zaben shugaban kasa - INEC

Hukumar shirya zabe mai zaman kanta ta kasa watau Independent National Electoral Commisslon (INEC) ta bada labarin cewa an yi zina da wasu ma'aikatan ta mata a yayin zabukan da aka gudanar satin da ya gabata na shugaban kasa da 'yan majalisar wakilai.

Wannan dai na kunshe ne a cikin wata sanarwar manema labarai da babban jami'in yada labarai da wayar da kan masu zabe na hukumar Mista Festus Okoye ya fitar dauke da sa hannun sa.

Wata-sabuwa: An yi zina da ma'aikatan mu lokacin zaben shugaban kasa - INEC
Wata-sabuwa: An yi zina da ma'aikatan mu lokacin zaben shugaban kasa - INEC
Asali: UGC

KU KARANTA: Dan takarar gwamna ya fatattaki 'yan gudun hijira a gidan shi

A cikin sanarwar, Mista Festus Okoye ya bayyana cewa duk da dai zaben da aka gudanar a iya cewa an yi shi ne cikin lumana a dukkan fadin kasar, amma dai hukumar ta dan samu tsaiko a wasu wuraren yayin zaben.

Ya ciga da cewa hukumar ta Independent National Electoral Commisslon (INEC) ta samu labarin tashe-tashen hankula da satar mutane da yiwa jami'an su fyade da ma rasa rai a wasu wuraren.

Haka zalika Mista Festus ya kuma yi anfani da damar wajen jajantawa iyalan wadanda suka rasa rayukan su ko jikkata koma rasa dukiya a wasu wuraren tare da basu hakuri da kuma tabbacin karin matakan tsaro daga hukumar domin kaucewa kara aukuwar lamarin a gaba.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma legit.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun labarai a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://web.facebook.com/legitnghausa?_rdc=1&_rdr

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.com

Asali: Legit.ng

Online view pixel