Kai-tsaye: Yadda zaben shugaban kasa da 'yan majalisun tarayya ke gudana a Katsina
Kai-tsaye: Yadda zaben shugaban kasa da 'yan majalisun tarayya ke gudana a Katsina
A kwana-a-tashi, masu iya magana suka ce wai jariri ango ne. Yau dai ga mu Allah ya kawo mu ranar da daukacin 'yan Najeriya ke ta tsumayen jira ta zabukan gama gari a daukacin fadin kasar.
A yau dai ana sa ran 'yan Najeriya a dukkan sako da lungun kasar za su jefa kuri'un su domin zabar shugaban kasa da kuma 'yan majalisun tarayyar su da suka hada da Sanatoci da kuma 'yan majalisar wakilai.
Legit.ng Hausa ta dauri aniyar kawo maku yadda zaben ke tafiya kai tsaye a jihar Katsina da Zamfara.
- Jumillar masu kada kuri'a = 3,187,988
- 'Yan takarar shugabannin kasa masu karfi
* Atiku Abubakar na jam'iyyar PDP
* Muhammadu Buhari na jam'iyyar APC
- Yan takarar Sanatoci masu karfi
Shiyyar Katsina ta Arewa (Daura)
* Hon Mani Nasarawa a PDP
* Sanata Ahmad Babba Kaita a APC
Shiyyar Katsina ta tsakiya
* Hon. Hamisu Gambo na PDP
* Injiniya Barkiya na APC
Shiyyar Katsina ta kudu (Funtua)
* Alhaji Bello Mandiya na APC
* Hon Shehu Inuwa Imam
A jihar Zamfara kuma a 'yan takarar sun hada da
- Yan takarar Sanatoci masu karfi
Shiyyar Zamfara ta Arewa
* Tijjani Yahaya Kaura
* ALHAJI YA'U SAHABI a APC
Shiyyar Zamfara ta tsakiya
* MOHAMMED HASSAN na PDP
* ALIYU IKRA BILBIS na APC
Shiyyar Zamfara ta Yamma
* ABUBAKAR ABDUL'AZIZ YARI na APC
* LAWALI HASSAN ANKA na PDP
Zaben a tsafe ta jihar zamfara
Asali: Legit.ng