NBA ta yi Allah wadai da cin mutuncin Qur’ani a Zamfara, tace ya zama dole a hukunta wadanda suka aikata laifin

NBA ta yi Allah wadai da cin mutuncin Qur’ani a Zamfara, tace ya zama dole a hukunta wadanda suka aikata laifin

Kungiyar lauyoyin Najeriya reshen jihar Zamfara ta yi Allah wadai da rahoton cin mutuncin littafi mai tsarki wato Qur’ani a Gusau, sannan tayi kira ga bincike domin gano wadanda suka aikata laifin.

Kungiyar ta NBA a wani taron manema labarai a Gusau a ranar Litinin, 11 ga watan Fabrairu tace lamarin abun bakin ciki ne da damuwa.

Bello Galadi, Shugaban kungiyar, yace mambobin kungiyar sun sake duba lamarin a wani taro a ranar Asabar, 9 ga watan Fabrairu.

NBA ta yi Allah wadai da cin mutuncin Qur’ani a Zamfara, tace ya zama dole a hukunta wadanda suka aikata laifin
NBA ta yi Allah wadai da cin mutuncin Qur’ani a Zamfara, tace ya zama dole a hukunta wadanda suka aikata laifin
Asali: UGC

Shugaban kungiyar yace: “Mun yi Allah wadai da wannan lamari sosai. Wannan abu ya fara wuce gonad a iri, kamar yadda ya sa faruwa a lokutan baya, inda aka gano shafukan Al-Qur’ani a bayin wata makarantar gwamnati da ke Sabon gari, Gusau.

KU KARANTA KUMA: Zaben 2019 zai zamo zabena na 5 kuma na karshe, ba zan wofantar da kundin tsarin mulki ba - Buhari

“Abun bakin ciki ne ganin cewa yan kwanaki da suka gabata an sake ganin littafin mai tsarki a wani bayin wani asibiti da ke Gusau.”

Galadi ya bayyana cewa akwai bukatan a kara karfin bincike a kasar sannan cewa ayi gaggawan tsaurara mataka tsaro a jihar domin kamo wadanda suka aikata hakan.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma legit.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun labarai a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://web.facebook.com/legitnghausa?_rdc=1&_rdr

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng