Buhari zai kaddamar da rijiyoyin man fetur da aka samu a jihar Bauchi

Buhari zai kaddamar da rijiyoyin man fetur da aka samu a jihar Bauchi

Rahotanni da ku zuwa mana sun nunacewa hukumar kula da albarkatun man fetur na kasa (NNPC) ta fitar da sanarwan cewa gobe Asabar 2 ga watan Fabrairu, shugaba Muhammadu Buhari zai kaddamar da sabbin rijiyoyin men fetur da aka samu nasaran tonawa a jihar Bauchi.

An dai yi nasarar tono man ne a yankin kogin Kolmani dake karamar hukumar Alkaleri na jihar Bauchi.

Wannan shine karo na farko a tarihin duniya da aka yi nasarar tona rijiyoyin man fetur a yankin arewa.

Buhari zai kaddamar da rijiyoyin man fetur da aka samu a jihar Bauchi
Buhari zai kaddamar da rijiyoyin man fetur da aka samu a jihar Bauchi
Asali: Twitter

Wannan babban nasara da aka samu ya sa jihar Bauchi za ta shiga jerin jihohi masu arzikin man fetur a Najeriya.

KU KARANTA KUMA: Zaben 2019: Kiristoci sun yi wa Shugaba Buhari wa'azi mai ratsa zuciya

A wani lamari na daban, Dan takarar shugabancin kasa karkashin jam'iyyar PDP, Alhaji Atiku Abubakar yayi alkawarin karasa gadar Niger ta biyu matukar aka zabe shi.

Atiku, wanda yayi alkawarin a jiya yayi babban zagayen kamfen din shi a Onitsha, yace zai tabbatar da an gaggauta kammala gadar saboda matarshi daga birnin kasuwancin jihar Anambra take.

Yayi alkawarin tabbatar da kammaluwar tare da gyara tituna a yankin da taimakon mataimakin shi, Mr Peter Obi.

Idan ka na da wata shawara ko bukatar ba mu labari, a tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Ku same mu a https://www.facebook.com/legitnghausa

Ko a http://twitter.com/legitnghausa

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta LEGIT NG Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Shafin NAIJ Hausa ya koma LEGIT

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng