Yanzu Yanzu: Yan Shi’a sun toshe mashigin majalisar dokokin kasar
- Mambobin kungiyar yan Shi’a sun toshe babban mashigin majalisar dokokin kasar
- Yan Shi'an na zanga-zanga ne akan ci gaba da tsare shugabansu Ibrahim Zakzakky
- Shugaban nasu dai da matarsa na kulle kusan kimanin shekaru uku da suka gabata
Mambobin kungiyar yan uwa Musulmi na Shi’a sun toshe babban mashigin majalisar dokokin kasar.
Mambobin kungiyar na zanga-zanga ne akan ci gaba da tsare shugabansu Ibrahim Zakzakky.
Daruruwan yan Shi’an sun kai zanga-zangar nasu ne majalisar dokokin kasar, lamarin da ya tursasa jami’an tsaro da ke gadin yan majalisar dokokin rufe kofa.

Asali: Facebook
A baya mun dai ji cewa yan shi'ar sun a sahu inda suka yi kabbarar Sallah suna addu'o'i ga gwamnatin ta tarayya.
A farkon makon nan ne kotun dake sauraron karar da gwamnatin jihar Kaduna tashigar ta hana bada belin shi malamin na su, Shaikh Ibrahim Zakzaky da matarsa don samun damar neman lafiya.
KU KARANTA KUMA: Mambobin APC sun bawa hammata iska a harabar wata kotun tarayya
Tun farko dai, Lauyan su Shaikh Ibrahim Zakzaky da matarsa ya shaidawa kotun cewa “idon Shaikh Zakzaky daya tuni ya lalace sannan wanda ya ragema yana kan tabuwa, kuma matarsa akwai harsasai a jikinta wandanda ba'a cire ba."
SANARWA: Shafin jaridar NAIJ.com Hausa ya sauya suna zuwa Legit.ng Hausa. Muna fatan za ka ci gaba da kasancewa tare da Legit.ng Hausa don karanta labarai da dumi duminsu.
Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayarku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en
Ku biyo mu a shafukan mu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/legitnghausa
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Asali: Legit.ng