Yanzu-yanzu: Obasanjo, Jonathan, AbdulSalam, da sauransu sun halarci zaman shugabbanin Najeriya da Buhari ke jagoranta yanzu a Aso Villa
Shugaba Muhammadu Buhari da tsaffin shugabannin Najeriya yau Talata, 22 ga watan Junairu a fadar shugaban kasa dake birnin tarayya Abuja.
Shugaban kasa na jagorantan taron shugabannin Najeriya ne wanda ya kunshi dukkan tsaffin shugabannin kasa, tsaffin shugaban Alkalai, gwamnoni jihohi 36, shugaban majalisar dattawa, da wasu ministocin shugaba Buhari.
Tsohon shugaban kasa, Olusegun Obasanjo, wanda a ranan Lahadi ya caccaki shugaba Buhari da gwamnatinsa kuma ya zargesa kan shirin yin magudin zaben 2019 ya halarci wannan taro.
Rahoto ya nuna cewa shugaba Obasanjo ne ya gabatar da addu'an mabiya addinin Kirista yayinda kaddamar da taron sannan tsohon shugaban Alkalai, Muhammad Uwais, ya bada addu;an Musulmai.

Asali: Facebook

Asali: Facebook

Asali: Facebook

Asali: Facebook
KU KARANTA: Gwamnati tarayya ta bukaci shugaban Alkalai, Walter Onnoghen, yayi murabus
Sauran tsaffin shugabannin kasan da suka halarta sune tsohon shugaban rikon kwarya, Cif Ernest Shonekan; Janar Abdus Sallam Abubakar, da Goodluck Ebele Jonathan.
Janar Ibrahim Babangida da Janar Yakubu Gowon basu halarta ba.
Majalisar shugabannin Najeriya ya kunshi shugaban kasa, mataimakin shugaban kasa, shugaban majalisar dattawa, kakakin majalisar wakilai, dukkan tsaffin shugabannin kasa dake raye, tsaffin shugabannin alkalai dake raye, gwamnonin jihohin Najeriya da sauransu.
Among the governors who had arrived were those of Osun, Kebbi, Zamfara, Plateau, Ebonyi, Adamawa, Edo, Lagos, Niger, Borno, Ogun, Ekiti and Kogi states.
Daga cikin gwamnonin da suka halarta suna gwamnan Osun, Kebbi, Zamfara, Plateau, Ebonyi, Adamawa, Edo, Lagos, Niger, Borno, Ogun, Ekiti da Kogi
Abubuwan da za'a tattauna sune al'amarin mafi karancin albashi da kuma zaben 2019.
Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.
Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=ng.legit.hausa&hl=en
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/legitnghausa
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,
Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Asali: Legit.ng