Aljanna-mai-masoya-da-yawa: An bada hutu a jihar Borno saboda zuwan Buhari
Gwamnatin jihar Borno ta sanar da ranar Litinin, 20 ga watan janairu a matsayin ranar hutu ga dukkan ma'aikatan ta saboda zuwan da shugaba Buhari zai yi jihar domin yin kamfe din tazarcen sa a tare da magoya bayan sa a ranar.
Majiyar mu ta sanar da mu cewa gwamnatin jihar ta Borno ta bayyana a cikin sanarwar bayar da hutun cewa ta yi haka ne domin ta baiwa kowa damar yin tururuwa domin zuwa tarbar shugaban kasar idan ya zo.

Asali: Twitter
KU KATANTA: Da wuya in fadi zabe - Buhari
Mai karatu dai zai iya tuna cewa ranar Litinin din nan ne dai shugaban kasar ya tsara zuwa jihohin Yobe da Borno kuma ma tuni har shirye shiren tarbar sa sun kankama a dukkan jahohin.
Shugaban kasar dai yanzu haka yana zagayawa jiha jiha ne domin gudanar da gangamin yakin neman zaben sa a zabukan da za'a gudanar kwanaki kadan masu zuwa.
Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma legit.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.
Latsa wannan domin samun labarai a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://web.facebook.com/legitnghausa?_rdc=1&_rdr
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,
Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.com
Asali: Legit.ng