Zuwan Buhari Kaduna: Taron cincirindon dubban mutane sun gigita jam'iyyar APC

Zuwan Buhari Kaduna: Taron cincirindon dubban mutane sun gigita jam'iyyar APC

Jam’iyyar PDP da magoya bayan ta sun shiga cikin matsanancin rudani a jihar Kaduna ranar Juma’a ganin irin miliyoyin mutanen da suka yi tururuwa a garin domin yi wa shugaban Kasa Muhammadu Buhari Lale marhaba da zuwa garin Kaduna.

Babu masaka tsinke a ko ina a cikin garin Kaduna tun daga safiyar Juma’a har kusan misalin karfe 7 na yamma da aka kammala taron.

Zuwan Buhari Kaduna: Taron cincirindon dubban mutane sun gigita jam'iyyar APC
Zuwan Buhari Kaduna: Taron cincirindon dubban mutane sun gigita jam'iyyar APC
Asali: Twitter

KU KARANTA: Gwamna El-rufa'i yayi babban rashi

Sai da shugaba Buhari yayi kusan awa 3 daga filin jirgin Kaduna zuwa filin wasa na Ahmadu Bello a dalilin cinkoson mutanen da ke kokarin daga masa hannu da yi masa lale-lale barka da zuwa.

Wannan taro dai ya nuna cewa jam’iyyar APC da Buhari na nan daram-dam da karfin su a jihar Kaduna sannan kuma ya sa da yawa daga cikin ‘yan Jam’iyyar PDP fadawa cikin dimuwa da tsoro ganin irin wadannan mutane da suka halarci filin taron.

A wajen taron gwamnan jihar Kaduna ya tabbatar wa shugaban Kasa cewa a wannan karon, sai ya samu kuri’u fiye da wanda ya samu a zaben 2015 a jihar.

Daga nan sai ya roki jama’a da su yi wa Buhari ruwan Kuri’u a madadin kyautar ranar zagayowar haihuwar sa da zai kasance ranar 16 ga watan Faburairu ne da yayi dadidai da ranar zaben shugaban kasa.

Ana shi jawabin, shugaban Muhammadu Buhari,ya tabbatar wa mutanen jihar cewa gwamnatin sa za ta ci gaba da yi wa talakawa aiki babu kakkautawa.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma legit.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun labarai a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://web.facebook.com/legitnghausa?_rdc=1&_rdr

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.com

Asali: Legit.ng

Online view pixel