Da dumin sa: Gwamna El-rufai yayi rashin babban yayan sa
Gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasir El-rufai yayi babban rashin yayan sa kuma majibincin lamurran sa, AVM Aliyu Ahmed El-rufai mai ritaya da sanyin safiyar ranar Asabar.
Rahotanni sun bayyana cewa AVM Aliyu Ahmed ya rasu ne yana da shekaru 71 a duniya a wata asibin garin Abuja bayan ya sha fama da rashin lafiya.
KU KARANTA: Jahohin Najeriya 13 dake da arzikin zinare
Legit.ng Hausa ta samu cewa shi dai Yayan na El-rufai ya rasu ya bar 'ya'ya shidda da mata daya kuma za'a yi jana'izar sa a masallacin Sultan Bello a gariin na Kaduna bayan sallar La'asar.
Tuni dai majiyar daga cikin iyalan mamatan ta shaida mana cewa an taho da gawar sa daga asibitin zuwa gidan sa a Kaduna domin yi masa sutura.
Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma legit.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.
Latsa wannan domin samun labarai a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://web.facebook.com/legitnghausa?_rdc=1&_rdr
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,
Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.com
Asali: Legit.ng