Yan iska sun kai hari ga ayarin motocin dan takarar gwamnan APC a Taraba

Yan iska sun kai hari ga ayarin motocin dan takarar gwamnan APC a Taraba

- Wasu yan iska a Wukari, Taraba sun kai hari ga ayarin motocin dan takarar gwamna a jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a Taraba, Alhaji Sani Danladi

- Jakadan jumhuriyar Trinidad da Tobago, Alhaji Hassan Ardo na a wajen da aka kai hari inda aka kona motoci akalla 10

- Ba a san inda dan takarar gwamnan da wasu daga cikin aboka tafiyan nasa ba domin bayan afkuwar rikicin wasu sun tsere ciki Wukari da kuma hukumar yan sanda dake garin

Wasu yan iska a Wukari, Taraba a ranar Alhamis, 17 ga watan Janairu, sun kai hari ga ayarin motocin dan takarar gwamna a jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a Taraba, Alhaji Sani Danladi.

Haka zalika harda jakada jumhuriyar Trinidad da Tobago, Alhaji Hassan Ardo na a wajen da aka kai hari inda aka kona motoci akalla 10.

Legit.ng ta tattaro cewa Danladi, wanda a yanzu yake kan rangaji kamfen dinsa a yankin kudancin jihar, na a hanyarsa ta zuwa karamar hukumar Ibi lokacin da wasu matasa suka farma ayarin motocinsu a wani mararraba a Wukari.

Yan iska sun kai hari ga ayarin motocin dan takarar gwamnan APC a Taraba
Yan iska sun kai hari ga ayarin motocin dan takarar gwamnan APC a Taraba
Asali: Depositphotos

Sun yiwa mararrabar kawanya, wanda hakan ya tursasa ayari motocin rage gudu, sannan sai suka farma motocin da mutanen ciki inda aka raunata wasu da dama sannan aka sace motoci.

Ba a san inda dan takarar gwamnan da wasu daga cikin aboka tafiyan nasa ba domin bayan afkuwar rikicin wasu sun tsere ciki Wukari da kuma hukumar yan sanda dake garin.

KU KARANTA KUMA: Atiku ya zargi Buhari da yaki da yan adawa maimakon yaki da rashawa

Kakakin APC a jihar, Aaron Atimas, wanda ya kasance a wajen da abun ya faru ya zargi yan adawa da alhakin kai harin.

Kokarin da aka yi don jin bakin yan sanda a Wukari da kakakin yan sanda a Jalingo bai samu ba saboda ba a dauki wayoyinsu ba.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: : https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng