Buhari na shirin guje ma muhawarar yan takarar shugaban kasa - CUPP
- Jam’iyyar CUPP tace tana dauke da ingantattun bayanai game da yunkurin shugaban kasa Buhari na guje ma muhawarar yan takarar shugaban kasa da zai gudana a ranar Asabar
- Kakakin jam’iyyar Imo Uochinyere ya yi wannan zargin a wata sanarwa ga manema labarai a Abuja
- Ugochinyere yace ana yunkurin ne don guje ma ci gaba da fallasa Buhari bayan rashi kokarinsa a taron da ya gudana a daren ranar Laraba
Jam’iyyun adawa a karkashin kungiyar hadin gwiwa Coalition of United Political Parties (CUPP) a ranar Alhamis, 17 ga watan Janairu tace tana dauke da ingantattun bayanai game da yunkurin shugaban kasa Muhammadu Buhari don guje ma muhawarar yan takarar shugaban kasa da zai gudaa a ranar Asabar.
Kakakin jam’iyyar Imo Uochinyere ya yi wannan zargin a wata sanarwa ga manema labarai a Abuja.
Ugochinyere yace ana yunkurin ne don guje ma ci gaba da g]fallasa Buhari bayan rashi kokarinsa a taron da ya gudana a daren ranar Laraba.

Asali: Depositphotos
Ugochinyere ya tuna cewa a baya CUPP ta tayar da batu akan lafiyar tunani shugabann kasar sanan ta nemi wata tawaga ta kwararru su biciki dukkanin yan takarar shugaban kasar.
Yace bayyana kokarin Buhari a wajen taron ranar Laraban a matsayi wani annoba ga kasar wanda ya mayar da yan Najeria abun dariya a idon duniya.
KU KARANTA KUMA: Cibiyar kasuwanci na Amurka ta tabbatar da ganawa da Atiku
A baya mu ji cewa Shugaba kasa Muhammadu Buhari ya bayyana a jiya Laraba, 16 ga watan Janairu cewa ba zai iya amsa tambaya a kan harkallar Gwamnan Jihar Kano Abdullahi Ganduje ba.
Buhari ya yi wannan waskiyar ce a wani taron ganawa da shi, inda ya ce a yanzu maganar ta na a hannun kotu da majalisa, don haka magana a kan batun zai zama yi wa shari’a katsalandan.
Sannan kuma Buhari ya ce shi baida masaniya akan ko asarkala da siddabaru aka yi wa bidiyon Ganduje ko a’a.
Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.
Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: : https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/legitnghausa
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Asali: Legit.ng