Ranar hisabi: Kotu ta sa ranar da zata yanke hukuncin karar kwace kadarorin Uwar gidan Jonathan

Ranar hisabi: Kotu ta sa ranar da zata yanke hukuncin karar kwace kadarorin Uwar gidan Jonathan

Babbar kotun tarayya dake zaman ta a jihar Legas ta saka ranar 11 ga watan Fabreru a matsayin ranar da zata yanke hukunci akan karar dake gabanta ta kwace makudan kudaden da aka samu a cikin asusun ajiyar uwar gidan tsohon shugaban kasa Patience Jonathan.

Hukumar nan dake yaki da masu yiwa tattalin arzikin kasa zagon kasa, EFCC ce ta shigar da karar a kwanan baya inda ta bukaci kotun ta kwace kudaden daga hannun wadda suke tuhuma har sai an kammala sharia.

Ranar hisabi: Kotu ta sa ranar da zata yanke hukuncin karar kwace kadarorin Uwar gidan Jonathan
Ranar hisabi: Kotu ta sa ranar da zata yanke hukuncin karar kwace kadarorin Uwar gidan Jonathan
Asali: UGC

KU KARANTA: Maimuna Aliyu ta sake shiga sabuwar cakwakiyar kudi

Legit.ng Hausa ta samu cewa kudaden da ake tuhuma dai sun kai adadin $8,435,788.84 da kuma sama da Naira biliyan 7.35 a asusun ajiya 15 na Patience Jonathan din wanda ake kyautata zaton ta samu lokacin da ta rike mukamin Sakatariyar din din din a jihar Bayelsa.

Tun farko da Lauyan EFCC. Rotimi Oyedepo ke magana a gaban kotun, yace uwar gidan ta yi anfani ne da wata kungiya da ba ta gwamnati ba wajen karkatar da kudaden zuwa asusun ajiyar kashin kanta.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma legit.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun labarai a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://web.facebook.com/legitnghausa?_rdc=1&_rdr

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.com

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng