Zan ba mata da matasa ayyukan yi idan na zama shugaban kasa - Atiku

Zan ba mata da matasa ayyukan yi idan na zama shugaban kasa - Atiku

- Atiku Abubakar ya jadadda alkawarinsa na samar da ayyukan yi da dama ga mata da matasan da basu da aikin yi a fadin kasar idan aka zabe shi a matsayin shugaban kasa

- Dan takarar shugaban kasar yayi kirarin cewa sama da yan Najeriya miliyan 10 ciki harda mata da matasa ne suka rasa ayyukansu a sekaru uku da rabi da jam’iyyar APC ta yi a mulki

- Yace gwamnatin APC ta gaza cika alkawaran zaben da ta dauka a 2015 na yaki da rashawa, rashin tsaro da kuma tarin talauci a fadin Najeriya

Dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP), Alhaji Atiku Abubakar, ya jadadda alkawarinsa na samar da ayyukan yi da dama ga mata da matasan da basu da aikin yi a fadin kasar idan aka zabe shi a matsayin shugaban kasa.

Ya jadadda alkawarin nasa a ranar Laraba, 9 ga watan Janairu a Minna, yayin da yake jawabi ga magoya bayan jam’iyyar a wani gangami inda ya kuma baje koli akan bukatar yin ayyukan ci gaba a jihar Niger.

Zan ba mata da matasa ayyukan yi idan na zama shugaban kasa - Atiku
Zan ba mata da matasa ayyukan yi idan na zama shugaban kasa - Atiku
Asali: Twitter

Dan takarar shugaban kasar yayi kirarin cewa sama da yan Najeriya miliyan 10 ciki harda mata da matasa ne suka rasa ayyukansu a sekaru uku da rabi da jam’iyyar All Progressives Congress (APC) tayi a kasar.

Atiku yayi alkawarin samar da dama da ayyuka yi a kasar baki daya.

KU KARANTA KUMA: Sanata Shehu Sani ya zargi uwargidan Gwamna El-Rufai da kalaman kiyayya

Ya bayyana cewa ayyukan ci gaba da akayi a kasar da suka hada da makarantu, hanyoyi da asibitoci duk gwamnatin baya ta PDP ce tayi inda yayi kira ga yan Najeriya da suyi waje da jam’iyya mai mulki.

A cewarsa, gwamnatin APC ta gaza cika alkawaran zaben da ta dauka a 2015 na yaki da rashawa, rashin tsaro da kuma tarin talauci a fadin Najeriya.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=ng.legit.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng