An sake kai wani kazamin farmaki a wani kauyen jihar Zamfara

An sake kai wani kazamin farmaki a wani kauyen jihar Zamfara

Labarin da muke samu da dumin sa shine na wasu 'yan bindiga da suke kashe akalla mutum 15 a kauyen Magamin Diddi dake a cikin yankin karamar Hukumar Muradun ta jihar Zamfara dake Arewa maso yammacin Najeriya.

Bayanai daga majiyoyin mu da kuma wasu da lamarin ya auku a kan idon su sun ce 'yan bindigar sun auka kauyen ne bayan sallar azahar din ranar Asabar da ta gabata, inda kuma suka rika harbi kan mai uwa-da-wabi.

An sake kai wani kazamin farmaki a wani kauyen jihar Zamfara
An sake kai wani kazamin farmaki a wani kauyen jihar Zamfara
Asali: UGC

KU KARANTA: An gano kudin takalmin da Buhari ke sawa

Legit.ng Hausa ta samu kuma cewa abin takaicin shine har ya zuwa yanzu jami'an tsaro ko hukumomin da abun ya shafa a jihar ba su ce komai ba game da wannan al'amari.

Sai dai wani mutumin yankin da lamarin ya auku a kan idon sa ya ce mutanen kauyen da dama ne suka jikkata sakamakon harbe-harben da barayin suka yi tsawon lokaci ba tare da samun dauki daga jami'an tsaro ba.

Jihar Zamfara tana fama da hare-haren 'yan fashin shanu da masu satar mutane don neman fansa, wadanda suka tagayyara yanki wanda a jiya ma har mun kawo maku yadda wani Shehi Malamin addinin musulunci daga Kano ya yi kira ga shugaba Buhari ya kara tura jami'an tsaro a jihar.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma legit.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun labarai a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://web.facebook.com/legitnghausa?_rdc=1&_rdr

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.com

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng