Malamin Islamiyya ya yi lalata da yar shekara 8 a Kano
Rahotanni sun kawo cewa rundunar 'yan sandan Najeriya reshen jihar Kano ta damke wani malamin Islamiyya mai shekaru 41, akan zargin lalata wata karamar yarinya mai shekara takwas.
An dai tattaro cewa yarinyar ta kasance daga cikin wasu yara bakwai da aka dauke shi musamman don ya rika koyar da su ilimin addini a gidansu.
Kakakin rundunar yan sandan ta jihar Kano, Sufuritenda Magaji Musa Majiya ya bayyana cewa sun sami kwararan hujjojin gurfanar da malamin a gaban kuliya, kuma iyayen yarinyar sun yi tsayuwar daka a kan a bi masu hakki.

Asali: Depositphotos
Ya ce malamin ya yi amfani da wasu dubaru na janyo hankalin yarinyar har ya yi lalata da ita a bayan gidansu.
A wani lamari makamanccin haka, mun ji cewa wata Kotun Majistire ta bayar da umarnin garkame wasu Mutane biyu a gidan wakafi, Felix Omenihu da Rotimi Amodu, da su ka yi tarayya da juna wajen aikata mummunan laifi na yiwa yarinya 'yar shekara biyar fyade a jihar Legas.
KU KARANTA KUMA: Bamu karbi gudunmawar N10m daga Gwamna Ganduje ba – EFCC
Yayin zartar da umarnin, Kotun ta na zargin wannan Mutane biyu; Omenihu dan shekara 46 da kuma Amodu mai shekaru 39 da laifin aikatawa wannan yarinya mummunan fasadi mai zunubi na kololuwa.
Jami'in dan sanda mai shigar da kara, Benson Emueri, ya shaidawa kotun cewa ababen zargin biyu sun aikata wannan mummunan laifi a gida mai lamba 3 da ke hanyar Vincent a unguwar Morocco ta jihar Legas.
Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.
Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: : https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/legitnghausa
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Asali: Legit.ng