Hotunan hatsabiban 'yan aware na kungiyar IPOB da suka kashe jami'in 'yan sandan Najeriya
Rundunar jami'an 'yan sandan Najeriya a ranar Lahadin da ta gabata sun gurfanar da wasu mutane 'yan kungiyar 'yan aware din nan dake neman tabbatar da kafuwar kasar Biafra watau Indigenous People of Biafra, IPOB, da aka zarga da kashe jami'an su.
Kamar dai yadda muka samu, jami'an 'yan sandan sun bayyana cewa hatsabiban sun kashe masu jami'i ne mai suna Nkwo Nnewi a jihar Anambra a wani kauye da ake cewa Ughelli.

Asali: Twitter
KU KARANTA: Dalilin da ya sa na shiga harkar fim - Garzali Miko
Legit.ng Hausa ta samu haka zalika cewa a yayin artabun 'yan sandan da dakarun hatsabiban 'yan-awaren, wani Sajant ya rasa ran sa sannan kuma shugaban ofishin shiyyar da wasu mukarraban sa sun jikkata.
A wani labarin kuma, Rundunar sojin Najeriya ta sanar da hannan ta wasu tubabbun manyan mayakan 'yan ta'addan Boko Haram akalla 155 zuwa ga gwamnatocin jahohin Borno, Yobe da kuma Adamawa domin mayar da su cikin iyalan su.
Shugaban shirin rundunar sojin na horarwa tare da sake tsugunnar da 'yan ta'addan Manjo Janar Bamidele Shafa shine ya sanar da hakan lokacin da yake jawabi a wajen bikin mika tubabbun 'yan ta'addan a garin Gombe.
Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma legit.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.
Latsa wannan domin samun labarai a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://web.facebook.com/legitnghausa?_rdc=1&_rdr
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,
Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.com
Asali: Legit.ng