Buhari ya cancanci yin tazarce – Dan majalisar wakilai

Buhari ya cancanci yin tazarce – Dan majalisar wakilai

Alhaji Bello Dantani, wani dan majalisa mai wakiltan Argungu/Augie a jihar Kebbi a majalisar wakilai ya ce Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya cancanci tazarce biyo bayan tarin nasarorin da ya samu a mulkinsa.

Dantani ya bayyana hakan a wani hira da kamfanin dillancin labarai na Najeriya (NAN) a birnin Kebbi a ranar Juma’a, 23 ga watan Nuwamba.

Dan majalisan wanda yayi ganawar sirri da Gwamna Atiku Bagudu, yace lamarin tsaro da ya inganta a jihar na daya daga cikin manyan nasarori a gwamnatin Buhari.

Buhari ya cancanci yin tazarce – Dan majalisar wakilai
Buhari ya cancanci yin tazarce – Dan majalisar wakilai
Asali: Facebook

A cewarsa gwamnatin APC ta magance matsalar sosai ba da wasa ba ba wai a jihar Kebbi kadai ba harma da jihohin arewacin kasar da dama.

KU KARANTA KUMA: Yanzu Yanzu: Buhari na ganawa da shugabannin APC a Benue

Dantani yayi watsi da zargin jam’iyyun adawa na cewa babu wani ci gaba da aka samu a fannin tsari a fadin kasar.

Dan majalisan yayi kira ga mutanen mazabarsa da su fito kwan su da kwarkwata domin marawa APC baya domin ganin ci gaban kasar a 2019.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma Legit.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=ng.legit.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng