Cikin hotuna: An shiga filin daga, Buhari ya kaddamar yakin neman zaben 2019
Shugaba Muhammadu Buhari ya kaddamar da yakin neman zaben kujeran shugaban kasa a zaben 2019 a yau Lahadi, 18 ga watan Nuwamba, 2018 a farfajiyar taro na fadar shugaban kasa.
Shugaban kasan ya yi kira ga yan siyasa da su gudanar da yakin neman zabe da zaman lafiya kuma kada su birkita kasa.
Buhari ya ce gwamnatinsa ta samu nasarori daban-daban cikin shekaru ukun da tayi kuma tana sa ran cigaba da hakan idan aka zabe shi.

Asali: Twitter
Yace: "Ina sane cewa an fara yakin neman zaben majalisar dokokin tarayya da na shugaban kasa a yau, ina kira ga yan takara su gudanar yakin neman cikin zaman lafiya,"
"Bamu da wata kasa face Najeriya, ba zamu banka mata wuta ba saboda siyasa."
KU KARANTA: Kada ku zabi APC, Atiku ya bukaci jama’ar yankin Arewa maso gabas

Asali: Facebook
Mun kawo muku rahoton cewa shugaba Muhammadu Buhari zai bayyana yadda yakin neman zabensa zai kasannce da taken ‘Next Level’ tsakanin karfe 5 zuwa karfe 8 a fadar shugaban kasa Abuja.
Hukumar gudanar da zabe ta kasa mai zaman kanta wato INEC ta baiwa jam’iyyun siyasa daman fara yakin neman zaben shugaban kasa da yan majalisan dokokin tarayya daga Yau Lahadi, 18 ga watan Nuwamba 2018.
Kakakin kwamitin yakin neman zaben shugaba Muhammadu Buhari, Festus Keyamo, ya ce wannan takarda da Buhari zai gabatar na daga cikin takardu guda biyu da bayyana domin fara yakin neman zaben.

Asali: Twitter
Sanarwa: Shafin Naij.com Hausa shine yanzu ya koma Legit.ng Hausa, don inganta muku zafafan labarai dama kayatarwa
Latsa wannan domin samun labarai a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/hausa.legit.ng
Twitter: https://twitter.com/hausa.legit.ng
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,
Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.com
Asali: Legit.ng