Bidiyon Ganduje na cin hanci: Lauya ya bukaci kotu da ta dakatar da majalisar dokoki
- An bukaci babbar kotun tarayya a Kano da ta dakatar da majalisar dookin jihar Kano daga ci gaba da binciken zargin cin hanci da ake yi wa gwamna Abdullahi Ganduje
- Abubakar Sani, lauya mazaunin Abuja ne ya nemi hakan a ranar Juma’a, 9 ga watan Nuwamba
- Sani a takarda mai lamba FHC/KN/CS/167/2018 ya ce majalisar dokokin jihar Kano bata da ikon gudanar da iurin wannan bincike akan gwamnan
Wani lauya mazaunin Abuja ya bukaci babbar kotun tarayya a Kano da ta dakatar da majalisar dookin jihar Kano daga ci gaba da binciken zargin cin hanci da ake yi wa gwamna Abdullahi Ganduje.
Abubakar Sani a takarda mai lamba FHC/KN/CS/167/2018 ya ce majalisar dokokin jihar Kano bata da ikon gudanar da iurin wannan bincike akan gwamnan.
Punch ta ruwaito cewa Sani ya kuma bukaci kotu da ta yi umurnin cewa kotun Code of Conduct Bureau ce kadai zata iya gudanar da irin wannan bi9ncike akan gwamnan bisa ga kundin tsarin mulki.

Asali: Depositphotos
Da yake nuni ga sashi 6 (1)&(2), 12 kotun da’ar ma’aiktan gwamnati a sashi na 1 ckin 5 ba kundin tsarin mulkin Najeriya, 1999, Sani yace CCB ce adai kundin tsarin mulki ya amince ta binciki irin wannan zargi.
KU KARANTA KUMA: Sauya shekar yan majalisa: APC na fafutukar ganin ta ci gaba da kasance mafi rinjaye
Ya kuma bayyana cewa karar akan binciken gwamnan don jama’a ne.
Idan ka na da wata shawara ko bukatar ba mu labari, a tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Ku same mu a https://www.facebook.com/legitnghausa
Ko a http://twitter.com/legitnghausa
Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta LEGIT NG Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en
Shafin NAIJ Hausa ya koma Legit.ng Hausa
Asali: Legit.ng