Da dumin sa: Dan takarar shugaban kasa, Atiku Abubakar ya dawo gida daga Dubai
Da dumin sa yanzu labarin da ke iske mu na nuni ne da cewa dan takarar shugaban kasa a jam'iyyar adawa ta Peoples Democratic Party (PDP), Alhaji Atiku Abubakar ya dawo gida Najeriya daga kasar Dubai.
Atiku Abubakar din dai ya tafi kasar Dubai ne tare da tawagar sa kunshe da jama'a da dama magoya bayan sa da jam'iyyar Peoples Democratic Party, inda suka shafe kwanaki suna shirya yadda za su tunkari zaben 2019.

Asali: Twitter
KU KARANTA: Musulunci ya sama karuwa a garin Jalingo
Legit.ng Hausa ta samu cewa jirgin tsohon mataimakin shugaban kasar ya diro Najeriya ne da misalin karfe 12 na daren ranar Lahadi tare da mukarraban nasa.
A wani labarin kuma, Labarin da muka samu daga majiyar mu ta Blue Print, ya na nuni ne da cewa jim kadan bayan saukar jirgin dake dauke da dan takarar shugaban kasar Najeriya na jam'iyyar Peoples Democratic Party, Atiku Abubakar, jami'an tsaro suka shiga bincikar sa.
Tsohon kakakin jam'iyyar na APC, Mista Timi Frank wanda kuma ke cikin tawagar tsohon shugaban kasar shine ya bayyanawa majiyar ta mu hakan a garin Abuja, babban birnin tarayyar Najeriya.
Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma legit.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.
Latsa wannan domin samun labarai a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://web.facebook.com/legitnghausa?_rdc=1&_rdr
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,
Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.com
Asali: Legit.ng