Shugaban marasa rinjaye a majalisar dokokin Kano ya sauya sheka daga PDP zuwa PRP

Shugaban marasa rinjaye a majalisar dokokin Kano ya sauya sheka daga PDP zuwa PRP

Shugaban marasa rinjaye a majalisa kuma mamba mai wakiltan yankin Kura/Garun Malam a majalisar dokokin jihar Kano, Alhaji Abdullahi Muhammad-Chiromawa ya sauya sheka daa jam’iyyar PDP zuwa PRP.

Dan majalisan ya sanar da sauya shekarsa yayinda yake zantawa da manema labarai aranar Litinin, 5 ga watan Nuwamba a jihar Kano.

Muhammad-Chiromawa ya kuma sanar da cewar ya yi murabus daga matsayinsa na shugaban marasa rinjaye a majalisar dokokin jihar.

Shugaban marasa rinjaye a majalisar dokokin Kano ya sauya sheka daga PDP zuwa PRP
Shugaban marasa rinjaye a majalisar dokokin Kano ya sauya sheka daga PDP zuwa PRP
Asali: Depositphotos

A cewarsa ya yanke shawarar barin PDP zuwa PRP domin bin sahun ubangidansa a harkar siyasa wato Alhaji Salihu Sagir-Takai, wanda ya koma PRP a kwanan nan.

Ya yi bayanin cewa ya yanke shawarar ne saboda saba dokar da suka yiwa manyan jam’iyyun siyasa biyu katutu a jihar.

KU KARANTA KUMA: Atiku zai je kasar Amurka a karshen Nuwamba - Okupe

Ku tuna cewa tsohon mataimakin gwamnan jihar, Farfesa Hafiz Abubakar wanda yayi murabus daga matsayinsa zuwa PDP ya sake sauya sheka zuwa PRP a kwanan nan.

Idan ka na da wata shawara ko bukatar ba mu labari, a tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Ku same mu a https://www.facebook.com/legitnghausa

Ko a http://twitter.com/legitnghausa

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Shafin NAIJ.com Hausa ya koma Legit.ng Hausa

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng