An cafke kasurgumin kwarto da ya kware wajen zina da matan aure a Kano
Hukumar Hizbah dake da alhakin tabbatar da da'a a tsakanin al'umma ta jihar Kano dake a Arewa maso yammacin Najeriya ta sanar da samun nasarar cafke wani kasurgumin kwarto da ya shahara wajen yin lalata da matan aure.
Daya daga cikin kwamandojin Hizbah din kuma mai magana da yawun ta, Ustaz Salisu rijiyar Lemo shine ya sanar wa da al'umma hakan a cikin wani dogon rubutu da yayi a shafin hukumar na dandalin sadarwar zamani.

Asali: Depositphotos
KU KARANTA: Buhari ya ba surikin sa babban mukami a sirrance
Legit.ng Hausa ta samu cewa kasurgumin kwarton, wanda aka sakaya sunan sa kamar yadda hukumar ta Hizbah ta labarata, yana ikirarin bayar da maganin aljannu ne ga matan auren inda daga nan ne kuma yake anfani da wannan damar wajen labbatar su.
A wani labarin kuma, Wata tawagar dalibai daga jami'ar Ahmadu Bello University (ABU), Zaria - jihar Kaduna ta zama zakara a wajen wata muhimmiyar gasa ta baje kolin fasahohi karo na 7 da cibiyar habaka ilimin lissafi ta kasa ke shiryawa duk shekara watau Nigeria Universities Computer Programming Contest (NUCPC).
Mun samu cewa tawagar dalibai daga jami'ar fasaha ta garin Akure ce ta zo na biyu a gasar yayin da kuma jami'ar jihar Ebonyi ta zo na uku duk dai a gasar wadda a gudanar a garin Abuja, babban birnin tarayya.
Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma legit.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.
Latsa wannan domin samun labarai a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://web.facebook.com/legitnghausa?_rdc=1&_rdr
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,
Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.com
Asali: Legit.ng