Rayuwa kenan: Abokan tsohon gwamna Fayose sun guje shi bayan bayan ya shiga hannun hukuma
Kimanin kwanaki sama da uku kenan tun bayan da babbar kotun tarayya dake zaman ta a garin Legas ta bayar da tsohon gwamnan jihar Ekiti, Ayodele Fayose beli amma har yanzu bai samu ya cika sharuddan belin nasa ba.
Wannan dai ya faru ne sakamakon yadda abokan siyasar sa da kuma arziki a lokacin da yake kan mulki suka guje shi lokacin da ake neman wadan da za su tsaya masa - a cikon sharrudan bayar da belin sa.

Asali: Twitter
KU KARANTA: Annabin karya ya bulla a Najeriya
Legit.ng Hausa ta samu cewa har ya zuwa ranar Juma'a da rana dai tsohon gwamnan yana a hannun jami'an hukumar dake kula da gidajen yari na Najeriya ana ta neman wadanda za su sa hannu a matsayin wadanda suka tsaya masa amma hakan ta citura, zargin da mai taimakawa gwamnan akan harkokin yada labarai, Lere Olayinka ya karyata.
Idan mai karatu dai bai manta ba, Alkalin kotun tarayyar ya bayar da belin tsohon gwamna Fayose din ne akan kudi Naira miliyan 50 da kuma wasu mutane biyu da dukkan su suka mallaki Naira miliyan 50 din za su tsaya masa kafin a sake shi.
Latsa wannan domin samun labarai a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://web.facebook.com/legitnghausa?_rdc=1&_rdr
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,
Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.com
Asali: Legit.ng