Yanzu Yanzu: Rundunar soji sun kashe yan ta’addan Boko Haram 2 sun kuma kwato makamai (hotuna)
Rundunar sojin bataliya 122 a Gwoza sun gwamza da wasu yan ta’addan Boko Haram a tashar sojoji na Kasasewa da ke jihar Borno a ranar 25 ga watan ktoba da misalin karfe 10:00 na dare.
A karshen arangaman sun yi nasarar kashe ýan ta’addan guda biyu yayinda wasu suka tsere da harbin bindiga.

Asali: Twitter
Kayayyakin da aka kwato sun hada da bindigogin AK47 guda uku dauke lamba 07042452, 56-35205749, 692530, mujalla uu, alburusai na musamman wanda ya kai tsawon 7.62MM da kayyakin sanyawa anda aka lalata.

Asali: Twitter
Ana ci gaba da kakkana a yankin. Kwamandan sashi na 7 Birgediya Janar Bulama Biu ya yaba ma rundunar sannan ya bukaci da su ci gaba da kula a koda yaushe.
KU KARANTA KUMA: Daliban jami’ar Afrika ta Kudu sun kera wani bulo daga fitsarin dan Adam
A wani lamari na daban legit.ng ta rahoto cewa Sojojin Nageriya sun samu gano gawar tsohon soja mai suna Major General Idris Alkali.
Manjo Janar Benson Akinroluyi ne ya bayyana haka ne a ranar Juma'a a jahar Plateau.
Yace "an kashe General Alkali ne sannan aka jefashi cikin wani rami mara zurfi a wata unguwa da akafi sani da "No man's land" a cikin Jos.
Idan ka na da wata shawara ko bukatar ba mu labari, a tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Ku same mu a https://www.facebook.com/legitnghausa
Ko a http://twitter.com/legitnghausa
Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta LEGIT NG Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en
Asali: Legit.ng