Wasu tsinannun barayi sun sace takalman Annabi Muhammadu SAW a Fakistan

Wasu tsinannun barayi sun sace takalman Annabi Muhammadu SAW a Fakistan

- Wasu tsinannun barayi sun sace takalman Annabi Muhammadu SAW

- A kasar Fakistan ne suka sace takalman

- An dai kafa kwamitin da zai yi bincike kan hakan

Kimanin shekaru 16 da suka gabata, an samu aukuwar wata irin sata mai ban takaici da ban mamaki a kasar Fakistan inda wasu suka sace takalman da ake kyautata zaton su ne fiyayyen halitta, Annabi Muhammadu SAW yayi anfani da su a lokacin rayuwar sa.

Wasu tsinannun barayi sun sace takalman Annabi Muhammadu SAW a Fakistan
Wasu tsinannun barayi sun sace takalman Annabi Muhammadu SAW a Fakistan
Asali: Facebook

Kamar dai yadda muka samu, barayin dai sun sace takalman ne a ranar 30 ga watan Yuli, 2002 a inda suke aje masallacin Badshahi a can kasar ta Fakistan.

Legit.ng Hausa dai sun samu cewa takalman na manzon Allah sun kasance a kasar ta Fakistan da dadewa kuma al'ummomi daga kasashe daban daban kan zo domin ganin takalman .

Yanzu dai haka wani alkali a kasar ya sa an kafa kwamitin bincike na musamman da nufin binciko barayin da ya ce sun tafka abun kunyar da ba'a taba yi ba a tarihin duniya.

Haka ma dai tuni har an saka gagarumar kyauta ta Dalar Amurka dubu 15 ga dukkan wanda ya bayar da cikakken bayanai game da yadda za'a gano barayin.

Latsa wannan domin samun labarai a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://web.facebook.com/legitnghausa?_rdc=1&_rdr

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.com

Asali: Legit.ng

Online view pixel