Yanzu Yanzu: Majalisar dokokin jihar Kano ta fara binciken bidiyon Ganduje

Yanzu Yanzu: Majalisar dokokin jihar Kano ta fara binciken bidiyon Ganduje

Majalisar dokokin jihar Kano ta bude shafin bincike akan bidiyon dake nuna gwamnan jihar, Abdullahi Ganduje na karban cin hanci wanda jaridar Daily Nigerian ta wallafa.

Da yake Magana akan cewa lamarin na bukatar duba na gaggawa a ranar Litinin, 15 ga watan Oktoba, wani mamba mai wakiltan mazabar Warawa, Labaran Madari yace majalisar dokokin tayi bincike domin sanin sahihancin bidiyon sannan ta dauki mataki.

Mista Madari yace bidiyon ya zub da kimar gwamnatin jihar, sannan kuma cewa don haka akwai bukatar ýan majalisa su dauki mataki na gaggawa.

Lamarin ya samu goyon baya daga Baffa DanÁgundi, wani mamba dake wakiltan wani bangare na Kano.

Yanzu Yanzu: Barazanar tsigewa yayinda majalisar dokokin jihar Kano ta fara binciken bindiyon cin hanci na Ganduje
Yanzu Yanzu: Barazanar tsigewa yayinda majalisar dokokin jihar Kano ta fara binciken bindiyon cin hanci na Ganduje
Asali: Depositphotos

Da yake martani kan lamarin, kakakin majalisa, Alhassan Rurum ya kafa kwamitin mutun bakwai don suyi bincike kan lamarin sannan su dawo wa majalisar da rahoto.

KU KARANTA KUMA: 2019: Buhari kainuwa ne dashen Allah – Kungiya

Mambobin kwamitin sun hada da Baffa DanÁgundi (Kano Municipal) a matsayin shugaba, Labaran Madari (Warawa) mamba; Garba Gafasa (Ajingi), mamba; and Zubairu Masu, (Sumaila) mamba.

Sauran sun hada da Ayuba Labaran (Kabo) mamba; Abubakar Galadima (Bebeji), mamba; Garba Yau Gwarmai (Kunchi/Tsanyawa), mamba da kuma; Mujtafa Amin, sakatare.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin Legit.ng Hausa zai koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewar ku tare da mu.

Idan ka na da wata shawara ko bukatar ba mu labari, a tuntube mu a labaranhausa@corp.legit.ng

Ku same mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa

Ko a http://twitter.com/naijcomhausa

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng