Saudiyya ta garkame Limamin Makkah da ya soki dokar halalta cakuduwan maza da mata a taruka

Saudiyya ta garkame Limamin Makkah da ya soki dokar halalta cakuduwan maza da mata a taruka

- Masarautar Saudiyya ta daure alkalin Shari'a a garin Makkah

- An kulle shafin Turanci da na Larabcin Sheik Talib na kafar Tuwita

Gwamnatin kasar Saudiyya ta damke wani babban limamin haramin Makkah kuma Alkali a Makkah, Sheikh Dr. Saleh al Taleb, bayan ya gabatar da Huduba da ya soki sabuwar dokar halatta cakuduwan maza da mata a taro a kasar.

Wata kungiyar fafutukua ta yanar gizo mai lura da cin zarafin malaman Saudiya da masu wa’azi da gwamnatin keyi mai suna Prisoners of Conscience,ta bayyana hakan a ranan Lahadi cewa an damke Sheikh Talib ne bayan gabatar da wannan hudubar.

Jaridar Khaleej ta bada rahoton cewa a hudubar, Sheik Talib, ya soki cakuduwa a iktiladi tsakanin maza da mata ajnibai a tarukan shakatawa da shirye-shirye.

Duk da cewa bai soki masarutar mulkin Saudiyya a hudubar ba, an damkeshi bayan masarautar ta samar da dokan halastawa mata halartan taruka a kasar.

Bayan haka kuma, an kulle shafin Turanci da na Larabcin Sheik Talib na kafar Tuwita.

Latsa wannan domin samun labarai a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/naijcomhausa

Twitter: https://twitter.com/naijcomhausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng