Yanzu Yanzu: Karya ne ba’a kara wa’adin hutun shugaba Buhari ba – Fadar shugaban kasa

Yanzu Yanzu: Karya ne ba’a kara wa’adin hutun shugaba Buhari ba – Fadar shugaban kasa

Fadar shugaban kasa tayi watsi da rade-radin dake yawo na cewa an kara wa’adin hutun shugaban kasa Muhammadu Buhari a Landan.

Fadar shugaban kasar ta yi jawabi a daren ranar Talata, 14 ga watan Agusta ta shafinta na Twitter, @NGRPresident, inda ta bayyana cewa akwai wani labara da jaridar Tribune na yanar gizo ta wallafa a ranar 5 ga watan Fabrairun 2017, “a yanzu wasu makirai na yayata labarin a shafukan zumunta, don haifar da rudani cewa yana da alaka da tafiyar shugaban kasar na yanzu.”

Yanzu Yanzu: Karya ne ba’a kara wa’adin hutun shugaba Buhari ba – Fadar shugaban kasa
Yanzu Yanzu: Karya ne ba’a kara wa’adin hutun shugaba Buhari ba – Fadar shugaban kasa

KU KARANTA KUMA: Bayan murabus din sa jam'iyyar PDP ta maye gurbin Sanata Akpabio

Fadar Shugaban kasar ta yi kira ga mutane da su “lura da shekarar labarin 2017.

“Shugaban kasar bai kara wa’adin hutun kwanaki 10 da ya tafi ba,” cewar fadar shugaban kasar.

Latsa wannan domin samun labarai a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/naijcomhausa

Twitter: https://twitter.com/naijcomhausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel