Rundunar sojin Saman Najeriya ta kara yaye matukan jiragen yaki

Rundunar sojin Saman Najeriya ta kara yaye matukan jiragen yaki

Rundunar sojin saman Najeriya Nigerian Air Force (NAF) a ranar Alhamis din da ta gabata ta kara yaye matukan jiragen yaki a makarantar koyon tukin jiragen dake a garin Kainji.

Da yake jawabi a wajen yaye daliban, Hafsan sojin saman kasar Air Marshal Sadique Abubakar da shugaban makarantar Air Vice Marshal Mohammed Idris ya wakilta ya bayyana yaye daliban a matsayin babban cigaba a kasar musamman ma wajen yaki da take yi da 'yan ta'adda.

Rundunar sojin Saman Najeriya ta kara yaye matukan jiragen yaki
Rundunar sojin Saman Najeriya ta kara yaye matukan jiragen yaki

KU KARANTA: EFCC ta biyo ta kan surukin Obasanjo

A wani labarin kuma, Mataimakin gwamnan jihar kaduna dake a Arewacin Najeriya, Barnabas Bantex a ranar Alhamis din da ta gabata ya bayyana kudurin sa na tsayawa takarar kujerar Sanatan jihar ta shiyyar kudancin ta a zaben 2019 mai zuwa.

Barnabas Bantex ya bayyana hakan ne lokacin da yake zantawa da manema labarai a garin na Kaduna inda ya bayyana cewa yanzu ya cimma daidaito tsakanin sa da gwamnan jihar game da kudurin nasa.

Latsa wannan domin samun labarai a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/naijcomhausa

Twitter: https://twitter.com/naijcomhausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel