Kai Tsaye: Yadda Zaben Gwamnan Jihar Ekiti ke Gudana, APC na Neman Kafa Tarihi

All posts
Key Events
Analysis
Exclusive
6 Posts
Sort by
Muhammad Malumfashi avatar
daga Muhammad Malumfashi

Kayan zabe sun ki isowa

Tuni dai an fara shirin sanin wanda zai zama gwamnan jihar Ekiti.

Masu kada kuri’a a karamar hukumar Afao-Ekiti a jihar Ekiti sun koka cewa an dade ba a kawo masu kayayyin zabe ba.

Kamar yadda The Nation ta rahoto, tsohon gwamnan Ekiti, Ayodele Peter Fayose ya fito ne daga garin Afao-Ekiti.

Muhammad Malumfashi avatar
daga Muhammad Malumfashi

BVAS ya ki aiki da kyau

A wani rahoton na The Nation har ila yau, an ji cewa wasu sun yi korafin cewa na’urar BVAS ba ta aiki da kyau a wajen zaben.

Sanata Babafemi Ojudu wanda ya taba zama Mai ba shugaban kasa Muhammadu Buhari shawara, yana cikin masu wannan koke.

Ahmad Yusuf avatar
daga Ahmad Yusuf

An fara kada kuri'a a mazabun jihar Ekiti

Karamar Hukuma (LGA): Ado

Wuri: Filin rukunin Chief Elerebi, daura da asibitin haihuwa d ke kan titin Okeyinmi.

Lambar mazaba: 06

Rumfar zabe: 013

Rahotanni sun nuna cewa an fara kada kuri'a, inda ake tantance masu zabe kafin a ba su damar jefa kuri'unsu a rumfar zabe ta 013 da ke mazaba ta 06 a karamar hukumar Ado.

Ekiti.
Yadda aka fara tantance masu kada kuri'a a rumfar zabe a jihar Ekiti Hoto: Ekiti News
Source: Facebook

Ahmad Yusuf avatar
daga Ahmad Yusuf

Hukumar INEC ta fara raba kayayyakin zabe

Jami'an zabe (SPO) da sauran ma'aikata wucin gadi, a yanzu haka sun fara jigilar kayayyakin zabe, wadanda suka hada da akwatunan zabe, rumfuna da kuma rijistar masu zabe zuwa wuraren da aka tura su.

Aikin na tafiya cikin tsari da kwanciyar hankali. Sai dai kuma, masu sanya idanu kan zaben sun lura cewa jami'an tsaro da ke wurin raba kayan ba su da yawa, domin kuwa 'yan sanda kadan ne aka tura.

Ahmad Yusuf avatar
daga Ahmad Yusuf

Mutane miliyan 1 ne zasu yanke hukunci a zaben Ekiti

Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa a Najeriya (INEC) ta sanar da kammala aikin raba katin zabe (PVC) cikin nasara domin gudanar da zaben gwamnan jihar Ekiti.

Kamar yadda jaridar The Guardian ta ruwaito, INEC ta bayyana cewa sama da masu zabe miliyan 1.02 ne suka karbi katunansu gabanin zaben gwamnan jihar Ekiti na shekarar 2026.

Muhammad Malumfashi avatar
daga Muhammad Malumfashi

EFCC sun dura rumfar zaben gwamna

Labari da dumin da aka samu yanzu shi ne jami’an EFCC sun je rumfar zaben gwamna Biodun Oyebanji a Ekiti.

An ga ma’aikatan hukumar a unguwar Ikogosi a Ekiti ta yamma sakamakon zargin da aka ji cewa ana sayen kuri’un jama’a.