Kai Tsaye: Yadda Zaben Gwamnan Jihar Ekiti ke Gudana, APC na Neman Kafa Tarihi
Kayan zabe sun ki isowa
Tuni dai an fara shirin sanin wanda zai zama gwamnan jihar Ekiti.
Masu kada kuri’a a karamar hukumar Afao-Ekiti a jihar Ekiti sun koka cewa an dade ba a kawo masu kayayyin zabe ba.
Kamar yadda The Nation ta rahoto, tsohon gwamnan Ekiti, Ayodele Peter Fayose ya fito ne daga garin Afao-Ekiti.
BVAS ya ki aiki da kyau
A wani rahoton na The Nation har ila yau, an ji cewa wasu sun yi korafin cewa na’urar BVAS ba ta aiki da kyau a wajen zaben.
Sanata Babafemi Ojudu wanda ya taba zama Mai ba shugaban kasa Muhammadu Buhari shawara, yana cikin masu wannan koke.
An fara kada kuri'a a mazabun jihar Ekiti
Karamar Hukuma (LGA): Ado
Wuri: Filin rukunin Chief Elerebi, daura da asibitin haihuwa d ke kan titin Okeyinmi.
Lambar mazaba: 06
Rumfar zabe: 013
Rahotanni sun nuna cewa an fara kada kuri'a, inda ake tantance masu zabe kafin a ba su damar jefa kuri'unsu a rumfar zabe ta 013 da ke mazaba ta 06 a karamar hukumar Ado.

Source: Facebook
Hukumar INEC ta fara raba kayayyakin zabe
Jami'an zabe (SPO) da sauran ma'aikata wucin gadi, a yanzu haka sun fara jigilar kayayyakin zabe, wadanda suka hada da akwatunan zabe, rumfuna da kuma rijistar masu zabe zuwa wuraren da aka tura su.
Aikin na tafiya cikin tsari da kwanciyar hankali. Sai dai kuma, masu sanya idanu kan zaben sun lura cewa jami'an tsaro da ke wurin raba kayan ba su da yawa, domin kuwa 'yan sanda kadan ne aka tura.
Mutane miliyan 1 ne zasu yanke hukunci a zaben Ekiti
Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa a Najeriya (INEC) ta sanar da kammala aikin raba katin zabe (PVC) cikin nasara domin gudanar da zaben gwamnan jihar Ekiti.
Kamar yadda jaridar The Guardian ta ruwaito, INEC ta bayyana cewa sama da masu zabe miliyan 1.02 ne suka karbi katunansu gabanin zaben gwamnan jihar Ekiti na shekarar 2026.
EFCC sun dura rumfar zaben gwamna
Labari da dumin da aka samu yanzu shi ne jami’an EFCC sun je rumfar zaben gwamna Biodun Oyebanji a Ekiti.
An ga ma’aikatan hukumar a unguwar Ikogosi a Ekiti ta yamma sakamakon zargin da aka ji cewa ana sayen kuri’un jama’a.