Kai Tsaye: Yadda Zaben Gwamnan Jihar Ekiti ke Gudana, APC na Neman Kafa Tarihi

All posts
Key Events
Analysis
Exclusive
14 Posts
Sort by
Our live updates have concluded for the day. Catch up on everything you missed below.
Ahmad Yusuf avatar
daga Ahmad Yusuf

Zaben Ekiti na tafiya cikin lumana - Yan sanda

Kwamishinan 'Yan Sanda da ke sanya idanu kan harkokin tsaro a zaben gwamnan Jihar Ekiti, Abayomi Shogunle, ya tabbatar da cewa ba a sami wani rahoton tashin hankali ba kawo yanzu.

Ya ce babu wani rahoto da ke nuna tursasawa ko tashin hankali tun bayan da aka fara gudanar da zaben a fadin jihar yau Asabar.

The Nation ta ve yayin da yake tattaunawa da manema labarai a garin Erijiyan-Ekiti, Shogunle ya bayyana zaben a matsayin mai cike da lumana.

Ya bayyana cewa masu zabe sun nuna da'a da kwanciyar hankali, yayin da hukumomin tsaro kuma suka baza jami'ansu sosai a daukacin runfunan zabe.

Ahmad Yusuf avatar
daga Ahmad Yusuf

Sanata Bamidele ya isa rumfar zabensa

Shugaban Masu Rinjaye na Majalisar Dattawan Najeriya, Opeyemi Bamidele, ya isa runfar zabensa domin kada kuri'a a zaben gwamnan jihar Ekiti da ke gudana.

A wani faifan bidiyo da The Nation ta wallafa, an ga magoya bayansa sun tarbe shi cikin murna da sowa yayin da ya wuce domin tantance shi kana ya jefa kuri'arsa kamar kowa.

Ibrahim Yusuf avatar
daga Ibrahim Yusuf

An yi wa direban dan takarar ADC duka

Dan takarar jam'iyyar ADC a Ekiti, Dare Bejide a bayyana cewa an yi wa direban shi duka yayin da ake zaben gwamna.

Ya ce:

"Sun yi wa direba na duka, sun masa jina-jina. sun ci zarafin jami'an tsaro na."
Ahmad Yusuf avatar
daga Ahmad Yusuf

Mataimakiyar gwamnan Ekiti ta kada kuri'a

Mataimakiyar Gwamnan Jihar Ekiti kuma 'yar takarar mataimakin gwamna ta APC. Cif (Mrs) Monisade Afuye, ta yaba wa masu zabe saboda nuna kishin kasa yadda suka fito domin kad kuri'a.

Haka zalika, Mrs Afuye ta jinjina wa Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) da kuma hukumomin tsaro bisa rashin nuna banbanci a zaben da ke gudana yau Asabar.

Mrs Afuye ta bayyana haka ne yayin da take kada kuri'arta a runfar zabe ta 003, da ke mazabar Atiba/Aafin 1, a garin Ikere Ekiti.

Mataimakiyar gwamnan Ekiti.
Mataimakiyar gwamnan jihar Ekiti, Monisade Afuye yayin da take kada kuri'a a mazabarta Hoto: Monisade Afuye
Source: Facebook

Abdullahi Abubakar avatar
daga Abdullahi Abubakar

Mazauna jihar Ekiti sun yaba da zabe cikin lumana

Yayin da jefa kuri’a ke ci gaba a zaben gwamnan Jihar Ekiti, wani mazaunin Ikere ya nuna godiya kan zaman lafiyar da aka samu a fadin jihar bayan kaɗa kuri’arsa.

“Mun gode wa Allah da zaben ya gudana cikin zaman lafiya” — wani mazaunin Ekiti ya bayyana bayan ya kaɗa kuri’arsa.

The Nation ta ce ana ci gaba da gudanar da zaben cikin lumana a wurare da dama kamar yadda mutane suka tabbatar.

Sharif Lawal avatar
daga Sharif Lawal

Oyebanji ya aika sako

Dangane da matsalolin na'urar BVAS, Gwamna Biodun Oyebanji ya yi kira da a yi haƙuri da hukumar zaɓe, The Cable ta kawo rahoton.

“Komai yana tafiya daidai, kuma zaɓen yana gudana cikin lumana. Mutane suna cikin farin ciki, kuma fitowar masu zaɓe abin a yaba ne."
“Mun samu gamsuwa. Sai dai, ina buƙatar yin kira ga mutanenmu da su ci gaba da yin haƙuri da INEC."
“Za a gyara dukkan waɗannan matsaloli, kamar yadda INEC da kanta ta ba ni tabbaci.”

- Gwamna Biodun Oyebanji

Sharif Lawal avatar
daga Sharif Lawal

Gwamna Oyebanji ya isa rumfar zabe

Gwamna Biodun Oyebanji ya isa rumfar zaben domin kada kuri'arsa a zaben gwamnan jihar Ekiti, rahoton TheCable ya nuna hakan.

Zai kada kuri'a ne a PU03, Ward 6, karamar hukumar Ekiti ta Yamma.

Sharif Lawal avatar
daga Sharif Lawal

Fayose ya kada kuri'a, ya hango nasarar Oyebanji

Tsohon gwamnan jihar Ekiti, Ayodele Fayose, ya ce nasarar Gwamna Biodun Oyebanji kusan tabbatacciya ce.

Fayose ya zanta da manema labarai bayan ya kaɗa ƙuri'arsa a garin Afao-Ekiti, da ke Ƙaramar Hukumar Irepodun/Ifelodun a jihar Ekiti, cewar rahoton TheCable.

“Oyebanji ya riga ya lashe zaɓen nan. Idan ka dubi yadda abubuwa suke tafiya a jihar nan da kuma yanayin yadda mutane ke nuna goyon bayansu, ina hasashen gagarumar nasara a gare shi.”

- Ayodele Fayose

Muhammad Malumfashi avatar
daga Muhammad Malumfashi

Kayan zabe sun ki isowa

Tuni dai an fara shirin sanin wanda zai zama gwamnan jihar Ekiti.

Masu kada kuri’a a karamar hukumar Afao-Ekiti a jihar Ekiti sun koka cewa an dade ba a kawo masu kayayyin zabe ba.

Kamar yadda The Nation ta rahoto, tsohon gwamnan Ekiti, Ayodele Peter Fayose ya fito ne daga garin Afao-Ekiti.

Muhammad Malumfashi avatar
daga Muhammad Malumfashi

BVAS ya ki aiki da kyau

A wani rahoton na The Nation har ila yau, an ji cewa wasu sun yi korafin cewa na’urar BVAS ba ta aiki da kyau a wajen zaben.

Sanata Babafemi Ojudu wanda ya taba zama Mai ba shugaban kasa Muhammadu Buhari shawara, yana cikin masu wannan koke.

Ahmad Yusuf avatar
daga Ahmad Yusuf

An fara kada kuri'a a mazabun jihar Ekiti

Karamar Hukuma (LGA): Ado

Wuri: Filin rukunin Chief Elerebi, daura da asibitin haihuwa d ke kan titin Okeyinmi.

Lambar mazaba: 06

Rumfar zabe: 013

Rahotanni sun nuna cewa an fara kada kuri'a, inda ake tantance masu zabe kafin a ba su damar jefa kuri'unsu a rumfar zabe ta 013 da ke mazaba ta 06 a karamar hukumar Ado.

Ekiti.
Yadda aka fara tantance masu kada kuri'a a rumfar zabe a jihar Ekiti Hoto: Ekiti News
Source: Facebook

Ahmad Yusuf avatar
daga Ahmad Yusuf

Hukumar INEC ta fara raba kayayyakin zabe

Jami'an zabe (SPO) da sauran ma'aikata wucin gadi, a yanzu haka sun fara jigilar kayayyakin zabe, wadanda suka hada da akwatunan zabe, rumfuna da kuma rijistar masu zabe zuwa wuraren da aka tura su.

Aikin na tafiya cikin tsari da kwanciyar hankali. Sai dai kuma, masu sanya idanu kan zaben sun lura cewa jami'an tsaro da ke wurin raba kayan ba su da yawa, domin kuwa 'yan sanda kadan ne aka tura.

Ahmad Yusuf avatar
daga Ahmad Yusuf

Mutane miliyan 1 ne zasu yanke hukunci a zaben Ekiti

Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa a Najeriya (INEC) ta sanar da kammala aikin raba katin zabe (PVC) cikin nasara domin gudanar da zaben gwamnan jihar Ekiti.

Kamar yadda jaridar The Guardian ta ruwaito, INEC ta bayyana cewa sama da masu zabe miliyan 1.02 ne suka karbi katunansu gabanin zaben gwamnan jihar Ekiti na shekarar 2026.

Muhammad Malumfashi avatar
daga Muhammad Malumfashi

EFCC sun dura rumfar zaben gwamna

Labari da dumin da aka samu yanzu shi ne jami’an EFCC sun je rumfar zaben gwamna Biodun Oyebanji a Ekiti.

An ga ma’aikatan hukumar a unguwar Ikogosi a Ekiti ta yamma sakamakon zargin da aka ji cewa ana sayen kuri’un jama’a.