An sanar da ranar fara jigilar mahajjatan Najeriya zuwa kasa mai tsarki

An sanar da ranar fara jigilar mahajjatan Najeriya zuwa kasa mai tsarki

Hukumar nan dake da alhakin jin dadi da walwalar mahajjatan Najeriya mallakin gwamnatin tarayya watau National Hajj Commission (NAHCOM) a takaice ta saka ranar 21 ga wannan watan na Juli a matsayin ranar fara jigilar mahajjata zuwa kasa mai tsarki.

Wannan dai na kunshe ne a cikin wata sanarwa da jami'in hulda da jama'a na hukumar ya fitar wakilin wannan jaridar ya kuma gani.

An sanar da ranar fara jigilar mahajjatan Najeriya zuwa kasa mai tsarki
An sanar da ranar fara jigilar mahajjatan Najeriya zuwa kasa mai tsarki

KU KARANTA: "Jam'iyyar PDP tamkar aljannace a Najeriya"

Legit.ng ta samu cewa a cikin sanarwar, hukumar ta kuma bayyana ranar 18 ga wannan watan din dai a matsayin ranar rufe karbar kudin zuwa hajjin daga mahajjatan kasar.

A wani labarin kuma, Shugaban majami'un darikar Roman Katolika na garin Abuja, babban binin tarayya mai suna John Cardinal Olaiyekan ya bayyana cewa bishop-bishop din Najeriya tuni suka yanke kauna da samun shugabanci na gari daga shugaba Buhari.

John Cardinal ya bayyana hakan ne a garin Ilorin na jihar Kwara lokacin da yake zantawa da manema labarai jim kadan bayan kammala nadin shugaban majami'un Roman Katolikan jihar Bishop Paul Olawoore.

Latsa wannan domin samun labarai a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/naijcomhausa

Twitter: https://twitter.com/naijcomhausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel