R-APC ba kungiyar adawar jam’iyyar mu ba ce - APC

R-APC ba kungiyar adawar jam’iyyar mu ba ce - APC

Mallam Bolaji Abdullahi, babban sakataren labarai na jam’iyyar All Progressives Congress yace kungiyar sabuwar APC (R-APC) ba kungiyar adawar jam’iyya mai mulki ba ce ya kara da cewa har yanzu APC na nan a hade karkashin shugaban kasa Muhammadu Buhari.

Abdullahi yace kungiyar R-APC sun yi maja da jam’iyyun adawa gabannin zaben 2019.

A cewarsa: “Muna girmama yancin kowa na shiga duk kungiyar da yake so don haka, muna son sanar da cewa kungiyar da ake kira da R-APC ba kungiyar adawar jam’iyyarmu bace. Jam’iyyarmu APC na nan a hade karkashin jagorancin shugabankasarmu Muhammadu Buhari.

A baya Legit.ng ta rahoto cewa Alhaji Buba Galadima, shugaban kungiyar sabuwar APC (R-APC) ya shawarci shugaban kasa Muhammadu Buhari da ajiye kudirinsa na sake takara a 2019 saboda zai sha kashi.

R-APC ba kungiyar adawar jam’iyyar mu ba ce - APC
R-APC ba kungiyar adawar jam’iyyar mu ba ce - APC

Galadima, wadda kungiyarsa ta R-APC ta hade da sauran jam’iyyun siyasa a ranar Litinin, 9 ga watan Yuli, yace Allah ya kaddata cewa shugaba Buhari zai fadi a zaben 2019.

KU KARANTA KUMA: Bana tunanin sabuwar jam’iyyar da PDP ta kafa zata iya tunkudar da jam’iyya mai mulki – Balarabe Musa

Ya kuma yi zargin cewa mambobin kungiyar siyasar sa na fuskantar barzanar mutuwa tunda suka bar APC ta hanyar sakonni.

Latsa wannan domin samun labarai a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/naijcomhausa

Twitter: https://twitter.com/naijcomhausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng