Kotu ta gargadi sanata Misau akan yin maganganu a kafofin watsa labarai

Kotu ta gargadi sanata Misau akan yin maganganu a kafofin watsa labarai

- Kotu ta umarci sanata Misau ya daina magana a kafofin watsa labaru akan laifufukan da ake tuhumar sa a kotu

- An sake gurfanar da Sanata Misau a gaban kotun tarayya akan yiwa sfeto janar na ‘yansanda karya da daganta shi da dabu'un banza

Babban kotun birnin tarayya dake, Maitama Abuja, ta gargadi sanata mai wakiltar mazabar Bauchi na tsakiya, Isah Misau, akan yin magana a kafofin watsa labaru akan game da laifufukan da ake tuhumar sa a kotu.

Gwamnatin tarayya a ranar Litinin ta sake gurfanar da Sanata Misau a gaban kotun akan yiwa sfeto janar na ‘yansanda, Ibrahim Idris kazafi da zargin cin hanci da rashawa da sauran su.

Kotu ta gargadi sanata Misau akan yin maganganu a kafofin watsa labarai
Kotu ta gargadi sanata Misau akan yin maganganu a kafofin watsa labarai

Lauyan Sanata, Misau, Mista Paul Erokoro (SAN), ya ce sanata ba zai kara yin magana a kafofin watsa labaru game da laifufukan da ake tuhumar sa ba.

KU KARANTA : Manoma miliyan 12m suka samu aikin yi a cikin wannan lokaci - Lai Mohammed

“Amma kada a manta shi sanata na mai wakiltar jama;a da yawa,” inji lauyan.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/naijcomhausa

Twitter: https://twitter.com/naijcomhausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng