Wasikar Obasanjo: Wannan rashin mutunci ne, ya sabawa tunani – Farfesa Itse Sagay

Wasikar Obasanjo: Wannan rashin mutunci ne, ya sabawa tunani – Farfesa Itse Sagay

Shugaban kwamitin fadar shugaban kasa kan bada shawara akan rashawa, Farfesa Itse Sagay ya ce rashin mutunci ne tsohon shugaban kasa, Olusegun Obasanjo, ya cewa shugaba Muhammadu Buhari kada yayi takara zaben 2019.

Sagay ya yi kira ga Obasanjo wanda ya bukaci yin tazarce ya nuna girma ga shugaba Buhari.

Yace: “Na ga maganganun Obasanjo kuma abin ya bani mamaki, mutumin da yayi kokarin tazarce karo na uku amma yana cewa wani kada ya sake neman takara. Wannan abu ya sabawa hankali.

“Ya kamata Obasanjo yayi kokari ya ga mutuncin mutane. Ya yi nasara sosai, babban mutum ne kuma ina girmama shi. Amma ya koyi girmama wasu.”

“Ina ganin rashin mutunci ga mutumin da ya bukaci tazarce na uku ya baiwa wanda ke neman tazarce na biyu wannan shawara. Wannan bai dace ba.”

Wasikar Obasanjo: Wannan rashin mutunci ne, ya sabawa tunani – Farfesa Itse Sagay
Wasikar Obasanjo: Wannan rashin mutunci ne, ya sabawa tunani – Farfesa Itse Sagay

Amma wani babban lauya kuma tsohon shugaba kungiyar lauyoyin Najeriya, Dr Olisa Agbakoba (SAN), ya ce babu abinda shugaba Buhari zai iya tsinanawa.

KU KARANTA: Jami’ar zata hukunta duk ɗalibin daya zazzago da wandonsa, da masu askin banza

Kana babban lauya, Femi Falana, ya siffanta wasikar Obasanjo a matsayin wa’azi ga shugaba Buhari. Ya bashi shawara ya kawar da miyagun da zagaye da shi.

Ku biyo mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa

ko a http://twitter.com/naijcomhausa

KU LATSA: Hanyar sauko da sabuwar manhajar jaridar Legit.ng Hausa cikin sauki

Ga masu shawara ko korafi, a same mu a labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng