Matan Sojoji sun cika da murna yayin da mazajensu suka dawo daga jihar Borno lafiya (Hotuna)

Matan Sojoji sun cika da murna yayin da mazajensu suka dawo daga jihar Borno lafiya (Hotuna)

- Rundunar Sojin Najeriya ta mayar da wasu sojoji gida daga filin daga

- An kwashe Sojojin ne da suka dade suna fafatawa da yan Boko Haram

A kokarinta na tabbatar da an sauya ma Sojojin da suka dade a bakin daga suna yaki da mayakan yan ta’adda wurin aiki, rundunar Soji ta mayar da wasu Sojoji barikinsu dake fatakwal.

Sojojin da suka fito daga bataliya ta 29 sun koma gida ne biyo bayan wani umarni da babban hafsan Sojin kasa, Laftanar Tukur Yusuf Buratai ya bayar da a sada su da iyalinsu, wanda hakan yayi matukar faranta musu rai.

KU KARANTA: Fin ƙarfi: Yadda wani fasinja ya suburbuɗi direba a cikin motarsa kuma ya hana shi kuɗin mota

Sojojin na daga cikin wadanda suka rayu bayan kwashe shekaru da dama suna yaki da yan ta’adda, a jawabinsa, kwamandan runduna ta 6, Manjo janar EO Udoh yayi ma Sojojin maraba da dawowa gida, sa’annan ya jinjina musu.

Matan Sojoji sun cika da murna yayin da mazajensu suka dawo daga jihar Borno lafiya (Hotuna)
Matan Soja

Legit.ng ta ruwaito kwamandan ya bukaci da su taya abokanan aikinsu da suke bakin fama da addu’a domin samun nasara akan yan Boko haram, sa’annan ya shawarce su dasu dage wajen bada gudunmuwa a duk lokacin da aka kiraye su.

Ga sauran hotunan:

Matan Sojoji sun cika da murna yayin da mazajensu suka dawo daga jihar Borno lafiya (Hotuna)
Matan Soja

Matan Sojoji sun cika da murna yayin da mazajensu suka dawo daga jihar Borno lafiya (Hotuna)
Soja da matarsa

Matan Sojoji sun cika da murna yayin da mazajensu suka dawo daga jihar Borno lafiya (Hotuna)
Sojojin da suka dawo

Ku biyo mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa

ko a http://twitter.com/naijcomhausa

Ga masu shawara ko korafi, a same mu a labaranhausa@corp.legit.ng

Tsohon soja yace kada ayi yaki, kalla:

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng