Ana neman taimako ‘yan Najeriya fisabilillah

Ana neman taimako ‘yan Najeriya fisabilillah

- Ana neman taimakon al’umma domin ceto wannan bawan Allah daga masalar rashin lafiyar da yake fama da

- Wannan mutumin dai na fama da matsanaicin ciwon kansa na saifa

- Ana bukata akalla kudin naira miliyan 3 don masa aiki da sayen magani

'Yan uwa ana neman a taimaka wa wannan bawan Allah domin ceto rayuwarsa.

Sunan sa Malam Muhammad Kasim dake gidan kanawa (Unguwar Kanawa) Kontagora Jihar Neja, yana fama da matsanaicin ciwon kansa na saifa, ankaishi asibitin Kwararru na Bida (Federal Medical Center Bida) inda likitoci suka aunashi suka tabbatar da ciwonsa yayi tsanani, yana bukatar ayi masa aikin gaggawa domin ceto rayuwarsa,

Kamar yadda Legit.ng ke da labari, kudin da ake bukata don masa aiki da sayen magani naira miliyan 3 gashi da iyali abunda ma zaici sai an taimaka masa.

Ana neman taimako ‘yan Najeriya fisabilillah
Malam Muhammad Kasim dake gidan kanawa wanda ke fama da matsanaicin ciwon kansa na saifa

Da wannan yake rokon gwamnati, da attajirai, da 'yan uwa da a taimakeshi domin ceto rayuwarsa alfarmar wannan wata na azumi mai falala da daraja.

Ana neman taimako ‘yan Najeriya fisabilillah
Takadar sayen magani da aka bashi a asibiti

KU KARANTA: Aiki sai mai shi: Gwamnatin jihar nan ta Arewa zata samar da guraben aiyuka 2000 ga matasa

Ga mai sha'awar taimaka masa ga account Number sa:

Suna: Muhammad Kasim

Banki:UBA Bank

Lambar Banki: 2010293197

Domin karin bayani za'a iya tuntubar lambar wayar dan uwansa dake jinyarsa : 08066551335

Allah yabada ikon taimakawa.

Ku biyo mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa

Ko a http://twitter.com/naijcomhausa

Ga bidiyon inda sunan Allah ya bayyana a jikin itacen moringa

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng