Shugaban kasar Senegal ya tafa ma Buhari a yadda ya shiga tsakani maganan Gambia

Shugaban kasar Senegal ya tafa ma Buhari a yadda ya shiga tsakani maganan Gambia

- Tsohon shugaban kasar Gambia Yahya Jammeh ya ki bada mulki ga Adama Barrow

- Amma shugabanni ECOWAS, a karkashin wahayin Shugaban kasar Buhari, sun nace Jammeh dole ne ya sallama

Shugaban kasar Senegal ya tafa ma Buhari a yadda ya shiga tsakani maganan Gambia
Shugaban kasar Senegal ya tafa ma Buhari a yadda ya shiga tsakani maganan Gambia

Legit.ng ya samu rahoto cewa Shugaban kasar Senegal, Macky Sall ya gode wa Shugaban kasar Muhammadu Buhari a yadda ya shiga tsakani rikicin ko rushewar Gambia da ya kai ga maido da dimokuradiyya a kasar ta yammacin Afirka.

KU KARANTA: Kasar nan na tafka mummunar asara - Sheik Pantami

Mai magana da yawun Shugaba Buhari, Mista Femi Adesina, ya bayyana haka a cikin wata sanarwa jiya.

Ya fada cewa: “Tsohon shugaban kasar Gambia Yahya Jammeh ya ki bada mulki ga Adama Barrow, wanda ya lashe zaben da aka gudanar a karshen watan Disamba, amma shugabanni ECOWAS, a karkashin wahayin Shugaban kasar Buhari, sun nace Jammeh dole ne ya sallama a watan Janairu. Ya yi a ranar, amma ba tare da son ran shi ba.”

KU KARANTA: Daga karshe, shugaba Buhari zai kai ziyara dajin Sambisa a ranar Litinin

Adesina ya ce shugaban Senegal kuma ya yi addu'a ga Allah ya baiwa shugaban kasar Buhari kiwon lafiya mai kyau da kuma samar da ƙarfi don gudanar da aikinsa.

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng